ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Radda Ya Amince Da Sakin ₦4bn Domin Ayyukan Al’umma A Gundumomi 361

by Sulaiman
1 month ago
Radda

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya amince da sakin Naira biliyan 4 domin aiwatar da kashi na biyu na Shirin Ci Gaban Al’umm, inda kowace daga cikin gundumomi 361 na jihar za ta karɓi Naira miliyan 10 domin gudanar da ayyukan da al’ummar yankin suka zaɓa bisa ga buƙatunsu.

Acikin sanarwar da Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Kaula Mohammed ya fitar ranar Laraba, 5 ga watan Agustan, ta bayyana cewa, an amince da hakan ne a taro na 12 na Majalisar Zartarwar Jihar Katsina na shekarar 2026, wanda aka gudanar a ranar Laraba a Gidan Gwamnatin Jihar. Da yake yi wa manema labarai bayani bayan kammala taron, Kwamishinan Yaɗa Labarai, Dakta Bala Salisu Zango, ya ce majalisar ta kuma amince da bayar da kuɗin tallafin haɗin gwiwa na shekarar 2026 domin aiwatar da Shirin ‘Nigeria for Women Project’, wanda ke da nufin bunƙasa tattalin arziƙin mata, ƙarfafa shigar su cikin harkokin kuɗi da inganta rayuwar iyalansu.

Majalisar ta kuma amince da bayar da kwangilar samar da kayayyakin fasahar sadarwa na zamani a sabbin Makarantun Sakandaren Misali da ke Jikamshi da Dumurkul. Aikin zai haɗa da azuzuwan zamani, allunan koyarwa na dijital da cibiyar sadarwa ta zamani domin inganta koyarwa da koyo.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, majalisar ta amince da wallafa rahoton ci gaban Shirin Gyaran Yanayin Kasuwanci na 2025 (BERAP), a ƙarƙashin Shirin SABER, domin ƙara inganta sauƙaƙe harkokin kasuwanci, ƙarfafa gyare-gyaren gwamnati da jawo masu zuba jari zuwa jihar.

A ɓangaren samar da ruwa, majalisar ta amince da sayo sinadaran tace ruwa na kashi na biyu na shekarar 2026 tare da tura motocin dakon ruwa domin ci gaba da samar wa mazauna birnin Katsina ruwa yayin da ake gudanar da aikin gyara da inganta cibiyar samar da ruwan jihar.

LABARAI MASU NASABA

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa waɗannan kudurori da aka amince da su, sun nuna ƙudirin Gwamna Radda na ci gaba da bunƙasa al’ummomi, ƙarfafa tattalin arziƙin mata, inganta ilimi, aiwatar da gyare-gyaren tattalin arziƙi da kuma tabbatar da samar da tsaftataccen ruwan sha ga al’ummar Katsina.

Radda
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang
  • Sulaiman
    Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris
  • Sulaiman
    Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu
  • Sulaiman
    Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

MASU ALAKA

Radda
Manyan Labarai

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Radda
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Radda
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Next Post
Sin Za Ta Tabbatar Da Kare Halaltattun Hakkoki Da Muradun Kamfanoninta

Sin Za Ta Tabbatar Da Kare Halaltattun Hakkoki Da Muradun Kamfanoninta

LABARAI MASU NASABA

Radda

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Radda

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Radda

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026
Radda

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.