Gwamnatin Jihar Kaduna ta amince da aiwatar da yarjejeniyar albashi na Gwamnatin Tarayya da aka cimma a watan Disambar 2025, tsakaninta da Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU) ga malaman Jami’ar Jihar Kaduna (KASU), inda za a fara biyan sabon albashin daga watan Oktoba 2026.
Kwamishinan Ilimi na jihar, Farfesa Abubakar Sani Sambo, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin wani taron manema labarai a Kaduna.
Ya ce amincewar ta biyo bayan rahoto da shawarwarin kwamitin tattaunawa mai mambobi tara da Gwamna Uba Sani ya kafa domin duba buƙatun ASUU-KASU da kuma samar da tsarin da ya dace wajen aiwatar da yarjejeniyar.
A cewarsa, tsarin da aka amince da shi ya yi daidai da yarjejeniyar FGN-ASUU ta 2025, ciki har da sabon tsarin CONUASS da sauran ƙarin albashi da alawus-alawus da suka shafi malaman jami’ar.
Kwamishinan ya ce matakin na daga cikin ƙudirin gwamnatin Uba Sani na fifita ilimi da bunƙasa ƙwarewar al’umma, inda ya bayyana cewa jihar ta ware akalla kashi 25 cikin 100 na kasafin kuɗinta ga ɓangaren ilimi tsawon shekaru uku a jere.













