Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya halarci taron kungiyar BRICS na 18 a birnin New Delhi na kasar India, inda ya gabatar da muhimmin jawabi.
A cewar shugaba Xi, kasar Sin za ta karbi shugabancin karba-karba na kungiyar a shekara mai zuwa.Ya kara da cewa, a bana ake cika shekaru 20 da kulla hadin gwiwar kungiyar BRICS. Kuma cikin shekaru 20 da suka gabata, tsarin hadin gwiwar kungiyar ya zama dandali mafi tasiri na hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa.
Ya ce, ya kamata kasashen su tsaya a bangare mafi dacewa na tahiri. Ya kuma yi kira ga kungiyar da ta jagoranci samar da ci gaba mai cike da kirkire-kirkire da jagorantar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma bunkasa koyi da juna tsakanin al’ummomi, har ma da jagorantar inganta tsarin shugabancin duniya.
Ya ci gaba da cewa, yayin da yanayin yankin Gabas ta Tsakiya da na Gulf ke sauyawa, yakin da ake yi a yankin ya haifar da asara mai tsanani ga jama’ar fadin yankin, kuma bai dace da muradun kasa da kasa ba.
Ya ce kasar Sin za ta hada hannu da kasashe mambobin BRICS wajen taka rawar da ta dace da samun zaman lafiya da lumana a yankin Gabas ta Tsakiya da yankin Gulf. (Fa’iza Mustapha)













