Wata ƴarkasuwa kuma shugabar ƙungiyar ‘Abba Kabir Yusuf Go Again’ na ƙaramar hukumar Fagge da ke Jihar Kano, Amb Adesuwa Ogechi Udu ta ce duk da cewa ita ƴar kasuwa ce ba ta shiga harkokin siyasa, amma duk da haka aikace-aikacen Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, yana matuƙar burge te, kuma duk wanda ya shigo jihar zai gasgata maganata, wadda ta ce za ta yi amfani da dukiyarta wajen samun nasarar gwamnan a zaɓen 2027.
Amb Adesuwa ta bayyan hakan ne a lokacin da take zantawa da manema labarai a ofishinta da ke Jihar Kano.Ta ce zuwa yanzu ta mayar da hankalinta wajen tallata kyawawan manufofin gwamnan ga matan ƙaramar hukumar, musamman matan da suke zaune a Unguwar Sabon Gari.
Ta ce ta yi imanin cewa al’ummar yankin maza da mata za su sake kaɗa wa gwamnan ƙuri’unsu a 2027.A cewarta, mataƙar al’ummar jihar suka sake bai wa gwamnan dama zai ɗora daga inda ya tsaya, idan kuma ba su sake ba shi dama ba, ba su san wanda za su zaɓa ya ci gaba da aikin alhairin da ya fara ba.Ta ce wasu daga ciki aikace-aikacen da gwamnan yake ci gaba da gunarwa a jihar sun haɗa da farfaɗo da harkar ilimi tare da ƙara malaman makarantu. Haka kuma ta ce ya gyara asibitocin jihar manya da ƙanana tare da wadata su da magunguna. Ta ce ya kuma gudanar da auren gata, sannan Gwamna Abba ya gyara hanyoyi a cikin unguwannin Sabon Gari da kuma tallafa wa ƙungiyoyi da jarin dogaro da kai. Daga ƙarshe, ta gode Allah da ake ƙara samun zaman lafiya a jihar da fatan za a ci gaba da addu’a.














