A yayin da zaɓukan 2027 ke ƙara ƙaratowa, gamayyar ƙungiyoyin da ke yaƙi da ɗumamar yanayi da masu kare rajin gurɓatar mahalli, sun ƙaddamar da wani shirin jan hankalin ƴan takara da su sanya tsare-tsaren yaƙi da ɗumamar yanayi a cikin jaddawalinsu na yaƙin neman zaɓe.Shugaban sashen samar da bayanai da tsare-tsare na ƙungiyar ƴan jarida da ke wallafa rahotannin yaƙi da ɗumamar yanayi, Kwamarade Ibrahima Yakubu, ya bayyana haka a madadin ƙungiyoyin a cikin sanarwar da ya raba wa manema labarai a Kaduna.
Ibrahima ya yi nuni da cewa, bai kamata ƴan takarar su rinƙa yi wa ɗumamar yanayi riƙon sakainar kashi ba a cikin ƙudurorinsu na yaƙin neman zaɓe, musamman duba da yadda batun ke ci gaba da zama barazana ga rayuwar miliyoyin ƴan ƙasar da kuma tattalin arzikinsu.
Ya ce ya zama wajbi ƴan takarar su sanya batun shirye-shiyen magance ɗumamar yanayi da kula da dashen itatuwa da maido da darajar gandun dazukan ƙasar nan da samar da makamashi da ingnanta aikin noma da sauransu.Ya ƙara da cewa wajibi ne ƴan takarar su sanya tsare-tsaren magance kwararowar hamada da gurɓatar ruwan sha da samar da wadataccen abinci mai gina jiki domin a ƙara inganta kiwon lafiyar ƴan ƙasar.
Ya kuma yi kira ga masu kaɗa ƙuri’a da su mara wa ƴan takarar da kawai suka sanya batun kare ɗumamar yanayi da kare gurɓatar muhalli a cikin ƙudurorinsu na yaƙin neman zaɓe.
A cewarsa, sanya batun na magance ɗumamar yanayi da kare gurɓatar muhalli a gaba hakan zai taimaka kan magance duk wasu ƙalubale da suka shafi ɗumamar yanayi da kare gurɓatar muhalli a cikin yankunansu.
Wannan shirin na samun tallafin ƙungiyoyin da ke da rajin yaƙi da ɗumamar yanayi da kuma shirin kare muhalli na MEI, bisa nufin ankarar da ƴan siyasa na su sanya tsare-tsaren yaƙi da ɗumamar yanayi a cikin jaddawalinsu na neman yaƙin neman zaɓe.














