Fitattun ’yan Nijeriya, ciki har da attajirin Afirka, Alhaji Aliko Dangote, Gwamnan Jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri da tsohon Gwamna Umar Jibrilla Bindow, sun halarci jana’izar tsohon gwamnan tsohuwar Jihar Gongola kuma tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na ƙasa, Alhaji Bamanga Muhammad Tukur, a Yola.
An gudanar da sallar jana’izar marigayin ne da misalin ƙarfe 11:00 na safe ranar Lahadi, 13 ga Satumba, 2026, a Masallacin Fadar Lamidon Adamawa da ke Yola, kafin daga bisani aka binne gawarsa a gidansa bisa tsarin koyarwar Musulunci.
Gwamna Fintiri ya jagoranci tawagar gwamnatin jihar, wadda ta haɗa da mambobin Majalisar Zartarwa, ’yan Majalisar Dokoki ta Jiha da ta Ƙasa, da manyan jiga-jigan PDP.
Haka kuma, jana’izar ta samu halartar ɗimbin sarakunan gargajiya da masu riƙe da sarautu, ƙarƙashin jagorancin Lamidon Adamawa, Mai Martaba Dr. Barkindo Aliyu Musdafa. Daga cikin waɗanda suka halarta akwai Sarkin Fofure, Ganwarin Masarautar Ganye da Ptil Madagali, tare da hakimai da sauran shugabannin al’umma daga ƙananan hukumomi 21 na jihar.
Alhaji Aliko Dangote ma yana cikin manyan waɗanda suka halarci jana’izar, tare da tsofaffin ministoci, sanatoci, ’yan kasuwa da manyan malaman addinin Musulunci.
Da yake bayyana rasuwar Tukur a matsayin babban rashi ga jihar da ƙasa, Gwamna Fintiri ya ce marigayin ya kasance uba, jagora kuma mai ba da shawara ga mutane da dama.
Fintiri ya ce, “Mun koyi abubuwa da dama daga gare shi. Rasuwarsa ta bar babban gibi wanda Allah kaɗai zai iya cikawa. Za mu ci gaba da yi masa addu’ar Allah Ya sa Aljanna ce makomarsa.”
Shi ma Dangote ya bayyana rasuwar Tukur a matsayin babban rashi ga Nijeriya, musamman ga ’yan kasuwa, tare da addu’ar Allah Ya yi masa rahama.
Bamanga Tukur ya rasu ne ranar Asabar a Abuja, kwanaki uku kacal kafin cika shekaru 91 da haihuwa.
Ya bar mata biyu da ’ya’ya 18, ciki har da Sakataren Gwamnatin Jihar Adamawa, Auwal D. Tukur.
Marigayin ya kasance fitaccen ɗan siyasa kuma dattijo mai kishin ƙasa, wanda ya taɓa zama Gwamnan tsohuwar Jihar Gongola, sannan ya taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasa da gudanar da ayyukan gwamnati a Nijeriya.
ADVERTISEMENT














