Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya sallami kwamishinoni shida daga muƙamansu a wani garambawul da ya yi wa Majalisar Zartarwar Jihar, da nufin ƙarfafa shugabanci da kuma samar da sabbin dabaru a gwamnatinsa.
Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG), Labaran Magaji, ne ya sanar da hakan yayin da yake ganawa da manema labarai bayan taron Majalisar Zartarwa da aka gudanar a Lafia.
Ma’aikatun da kwamishinonin da abin ya shafa ke jagoranta sun haɗa da Ma’aikatar Ayyuka, Harkokin Mata, Yaɗa Labarai, Filaye, Kimiyya da Fasaha, da kuma Ma’aikatar Tsaro da Sauran Harkoki.
Magaji ya ce an buƙaci kwamishinonin su sauka daga muƙamansu ne domin ba da damar shigowar sabbin dabaru da kuma sake tsara gwamnati domin inganta ayyukan yi wa al’umma hidima a sauran watannin wa’adin mulkin gwamnatinsa.
Sai dai ya jaddada cewa matakin ba yana nufin sun gaza wajen gudanar da aikinsu ba ne, yana mai cewa gwamnatin ta yaba da ƙwazo, ƙwarewa da gudunmawar da jami’an da abin ya shafa suka bayar a lokacin da suke kan muƙamansu.













