• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Nemi Karin Tallafi Ga Manyan Makarantun Jihar

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
Gwamna

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bukaci karin tallafi daga Asusun Tallafa wa Manyan Makarantu na TETFund, domin kammala wasu gine-ginen a manyan makarantun Jihar.

Gwamnan ya yi wannan roko ne a wata ziyarar aiki da ya kai hedikwatar Hukumar ta TETFUND a Abuja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa gwamnan ya bukaci tallafi, musamman ga Jami’ar Jihar Zamfara da kuma Kwalejin Fasaha ta Abdu Gusau.

  • Yadda Aka Gudanar Da ‘Tattakin Zaman Lafiya’ A Jihar Zamfara
  • Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da ‘Yan Bindiga

Ya kara da cewa, Jami’ar jihar da ke Karamar Hukumar Talatan Mafara tana da ayyuka da dama wadanda gwamnatocin baya suka fara kuma suka yi watsi da su.

“Lokacin da na ziyarci TETFund, na ambaci cewa a kullum neman kari muke yi. A yau, na zo ne don neman karin tallafi ga wasu manyan makarantun Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

“Na ziyarci Karamar Hukumar Talata Mafara makonni biyu da suka wuce na ga ayyukan da TETFUnd ta gudanar a Jami’ar Jihar Zamfara. Abin takaici, akwai ayyuka da yawa da aka yi watsi da su a zamanin gwamnatocin baya.

“Muna fuskantar matsaloli game da gyaran Kwalejin Fasaha ta Abdu Gusau, kuma ina bukatar goyon bayanku don warware wannan matsala.

“Zamfara na fama da kalubale daban-daban baya ga matsalar rashin tsaro. Lokacin da muka karɓi mulki a shekarar da ta gabata, ba a biya ma’aikata albashi ba na tsawon watanni uku, kuma dalibanmu ba su iya biyan kudin jarrabawar WAEC da NECO. Har ila yau, muna da dalibai da yawa a kan tallafin karatu a kasashen Cyprus, Indiya, da Sudan wadanda ba a kula da su ba, da sauran batutuwan gaggawa.

“Gwamnatina ta warware matsalar albashin ma’aikata, ta biya bashin da ake bi na WAEC da NECO, sannan ta sasanta tare da daidaita biyan daliban da za su samu tallafin karatu a kasashen waje. Mun zo nan ne domin neman taimakon ku, wanda zai taimaka sosai a kokarinmu na ceto da sake gina Zamfara.”

Da yake mayar da jawabi, Sakataren Zartarwa na Asusun, Arc Sonny T. Echono ya yaba wa Gwamna Lawal bisa nasarorin da ya samu a shekarar farko da ya yi kan mulki.

“Ina so in taya ka murnar cika shekara guda a kan karagar mulki, kuma ina so in yaba maka kan ayyukan da ka ke yi a ma’aikatun gwamnati, cibiyoyi, asibitoci, da sauran fannoni.

“Za mu sake duba bukatar gwamna, kuma mu yi duk mai yiwuwa. Yunkurin da ka ke yi wajen magance al’amuran jihar abin yaba wa ne kuma ya nuna babban matsayi, ni kaina ina so in gode maka kan daidaita bashin WAEC da NECO,” in ji Echono.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
Labarai

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar
Labarai

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Manyan Labarai

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
Next Post
Me Ya Sa Kamfanonin Waje Ke Neman Ci Gaba A Kasar Sin

Me Ya Sa Kamfanonin Waje Ke Neman Ci Gaba A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.