ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, December 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Nemi Karin Tallafi Ga Manyan Makarantun Jihar

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Gwamna

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bukaci karin tallafi daga Asusun Tallafa wa Manyan Makarantu na TETFund, domin kammala wasu gine-ginen a manyan makarantun Jihar.

Gwamnan ya yi wannan roko ne a wata ziyarar aiki da ya kai hedikwatar Hukumar ta TETFUND a Abuja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa gwamnan ya bukaci tallafi, musamman ga Jami’ar Jihar Zamfara da kuma Kwalejin Fasaha ta Abdu Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Aka Gudanar Da ‘Tattakin Zaman Lafiya’ A Jihar Zamfara
  • Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da ‘Yan Bindiga

Ya kara da cewa, Jami’ar jihar da ke Karamar Hukumar Talatan Mafara tana da ayyuka da dama wadanda gwamnatocin baya suka fara kuma suka yi watsi da su.

“Lokacin da na ziyarci TETFund, na ambaci cewa a kullum neman kari muke yi. A yau, na zo ne don neman karin tallafi ga wasu manyan makarantun Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin NMDPRA Da NUPRC Sun Yi Murabus Saboda Zargin Da Dangote Ya Yi Musu

PDP Ta Amince Da Jagorancin Turaki, Ta Ce Ta Shiga ‘Sabon Babin Haɗin Kai’

“Na ziyarci Karamar Hukumar Talata Mafara makonni biyu da suka wuce na ga ayyukan da TETFUnd ta gudanar a Jami’ar Jihar Zamfara. Abin takaici, akwai ayyuka da yawa da aka yi watsi da su a zamanin gwamnatocin baya.

“Muna fuskantar matsaloli game da gyaran Kwalejin Fasaha ta Abdu Gusau, kuma ina bukatar goyon bayanku don warware wannan matsala.

“Zamfara na fama da kalubale daban-daban baya ga matsalar rashin tsaro. Lokacin da muka karɓi mulki a shekarar da ta gabata, ba a biya ma’aikata albashi ba na tsawon watanni uku, kuma dalibanmu ba su iya biyan kudin jarrabawar WAEC da NECO. Har ila yau, muna da dalibai da yawa a kan tallafin karatu a kasashen Cyprus, Indiya, da Sudan wadanda ba a kula da su ba, da sauran batutuwan gaggawa.

“Gwamnatina ta warware matsalar albashin ma’aikata, ta biya bashin da ake bi na WAEC da NECO, sannan ta sasanta tare da daidaita biyan daliban da za su samu tallafin karatu a kasashen waje. Mun zo nan ne domin neman taimakon ku, wanda zai taimaka sosai a kokarinmu na ceto da sake gina Zamfara.”

Da yake mayar da jawabi, Sakataren Zartarwa na Asusun, Arc Sonny T. Echono ya yaba wa Gwamna Lawal bisa nasarorin da ya samu a shekarar farko da ya yi kan mulki.

“Ina so in taya ka murnar cika shekara guda a kan karagar mulki, kuma ina so in yaba maka kan ayyukan da ka ke yi a ma’aikatun gwamnati, cibiyoyi, asibitoci, da sauran fannoni.

“Za mu sake duba bukatar gwamna, kuma mu yi duk mai yiwuwa. Yunkurin da ka ke yi wajen magance al’amuran jihar abin yaba wa ne kuma ya nuna babban matsayi, ni kaina ina so in gode maka kan daidaita bashin WAEC da NECO,” in ji Echono.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin NMDPRA Da NUPRC Sun Yi Murabus Saboda Zargin Da Dangote Ya Yi Musu
Manyan Labarai

Shugabannin NMDPRA Da NUPRC Sun Yi Murabus Saboda Zargin Da Dangote Ya Yi Musu

December 17, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Labarai

PDP Ta Amince Da Jagorancin Turaki, Ta Ce Ta Shiga ‘Sabon Babin Haɗin Kai’

December 17, 2025
Bukukuwan Ƙarshen Shekara: NSCDC Ta Tura Jami’anta 4,000 Don Tsaro A FCT
Manyan Labarai

Bukukuwan Ƙarshen Shekara: NSCDC Ta Tura Jami’anta 4,000 Don Tsaro A FCT

December 17, 2025
Next Post
Me Ya Sa Kamfanonin Waje Ke Neman Ci Gaba A Kasar Sin

Me Ya Sa Kamfanonin Waje Ke Neman Ci Gaba A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Sun Jima Suna Kitsa Karairayi

Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Sun Jima Suna Kitsa Karairayi

December 17, 2025
Jami’ar Kasar Sin Ta Jaddada Adawar Kasarta Da Duk Wani Tsoma Baki Daga Sashen Waje Cikin Batun Yankin Taiwan

Jami’ar Kasar Sin Ta Jaddada Adawar Kasarta Da Duk Wani Tsoma Baki Daga Sashen Waje Cikin Batun Yankin Taiwan

December 17, 2025
Shugabannin NMDPRA Da NUPRC Sun Yi Murabus Saboda Zargin Da Dangote Ya Yi Musu

Shugabannin NMDPRA Da NUPRC Sun Yi Murabus Saboda Zargin Da Dangote Ya Yi Musu

December 17, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

PDP Ta Amince Da Jagorancin Turaki, Ta Ce Ta Shiga ‘Sabon Babin Haɗin Kai’

December 17, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Jinjinawa Sabon Matakin Bude Kofa Na Lardin Hainan Da Na Sin Baki Daya

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Jinjinawa Sabon Matakin Bude Kofa Na Lardin Hainan Da Na Sin Baki Daya

December 17, 2025
FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya

FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya

December 17, 2025
Bukukuwan Ƙarshen Shekara: NSCDC Ta Tura Jami’anta 4,000 Don Tsaro A FCT

Bukukuwan Ƙarshen Shekara: NSCDC Ta Tura Jami’anta 4,000 Don Tsaro A FCT

December 17, 2025
Wang Yi: Dole Ne A Magance Sake Aukuwar Munanan Hare-hare Da Japan Ta Taba Kaiwa Sassan Ketare A Tarihi 

Wang Yi: Dole Ne A Magance Sake Aukuwar Munanan Hare-hare Da Japan Ta Taba Kaiwa Sassan Ketare A Tarihi 

December 17, 2025
Bunkasar Masana’antun Kasar Sin Ya Kai Kaso 6.0% a Watanni 11 Na Farkon Shekarar Bana

Bunkasar Masana’antun Kasar Sin Ya Kai Kaso 6.0% a Watanni 11 Na Farkon Shekarar Bana

December 17, 2025
Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

December 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.