Hukumar Tsaro ta Farar Hula ta Nijeriya NSCDC, reshen Babban Birnin Tarayya FCT, ta tura “jami’anta 4,000 a fadin yankin don tabbatar da tsaro a yayin bukukuwan karshen shekara dake tafe.”
Kwamandan rundunar FCT, Olusola Odumosu, ya ba da umarnin tura jami’an a matsayin wani bangare na matakan kare rayuka da kadarori, da kuma kare kayayyakin more rayuwa kafin lokacin da kuma bayan lokacin bukukuwa.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Monica Ojobi ta sanya wa hannu kuma aka fitar a ranar Laraba.
Jami’an da aka zaɓo daga ɓangarori daban-daban na rundunar, an tura su ne zuwa yankuna daban-daban da ke cikin babban birnin na tarayya
ADVERTISEMENT














