Shugaba Bola Tinubu ya nemi Majalisar Dattawa ta amince da nadin sabbin manyan jami’ai guda biyu na Hukumar Kula da albarkatuj Man Fetur ta Kasa (NMDPRA) da kuma Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriya (NUPRC).
Bukatun sun biyo bayan murabus din ba zato ba tsammani na Injiniya Farouk Ahmed na NMDPRA da Gbenga Komolafe na NUPRC. Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ne ya nada dukkan jami’an biyu a shekarar 2021 don jagorantar hukumomin kula da harkokin man fetur guda biyu da Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA) ta kafa.
- Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Jinjinawa Sabon Matakin Bude Kofa Na Lardin Hainan Da Na Sin Baki Daya
- PDP Ta Amince Da Jagorancin Turaki, Ta Ce Ta Shiga ‘Sabon Babin Haɗin Kai’
Don cike wadannan mukamai, kakakin shugaban kasa, Bayo Onanuga, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba da yamma, ya ce Shugaba Tinubu ya rubuta wa Majalisar Dattawa, yana neman a gaggauta tabbatar da Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan a matsayin Shugaba na NUPRC da Injiniya Saidu Aliyu Mohammed a matsayin Shugaba na NMDPRA.
Wadanda aka nada guda biyu kwararru ne a fannin mai da iskar gas.
LEADERSHIP ta ruwaito cewa, a cikin makon nan ne, Attajirin Afirka kuma mamallakin matatar man fetur ta Dangote, Aliko Dangote ya tuhumi Ahmed da laifin almubazzaranci da cin hanci da rashawa.














