Gobe Alhamis 18 ga watan nan, muhimmiyar rana ce a tarihin ci gaban kasar Sin, domin kuwa shekaru 47 da suka gabata daidai da ranar ne cikakken zama na uku na kwamitin kolin JKS na 11, ya kafa tarihin kaddamar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofar kasar Sin ga duniya. Shekaru 47 bayan hakan kuma, za a fara aiwatar da matakan kwastam na musamman a dukkanin fadin yankin cinikayya cikin ’yanci na Hainan ko FTP, wanda hakan ya zamo sabon muhimmin mataki a manufar kasar Sin ta bude kofa bisa matsayin koli. Yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje, wadanda akan kira “juyin-juya-hali na biyu” na kasar Sin, sun ci gaba da sauya yanayin kasar Sin da ma duniya baki daya.
Sakamakon kuri’ar jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar domin jin mahangar al’ummun kasa da kasa, kaso 92.2 bisa dari sun amince cewa, gina yankin FTP na Hainan muhimmin mataki ne da Sin ta dauka, da zai fadada bude kofa bisa matsayin koli, da yaukaka budadden salon raya tattalin arzikin duniya. Kazalika, kaso 93 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin na ganin yankin FTP na Hainan, zai zamo muhimiyar kafa da Sin za ta yi amfani da ita wajen bude sabon zagayen manufar bude kofa ga duniya.
Kafar CGTN ta gudanar da kuri’ar jin ra’ayin jama’ar ne ta harsunan Turancin Ingilishi, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci, da harshen kasar Rasha, an kuma tattara ra’ayoyin mutane 4,190 cikin sa’o’i 12. (Saminu Alhassan)














