ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da ‘Tattakin Zaman Lafiya’ A Jihar Zamfara

Gwamna Dauda Ya Jaddada Cewa Babu Sulhu Da 'Yan Bindiga

by Leadership Hausa
2 years ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya sake jaddada cewa gwamnatin sa ba za ta taɓa shiga sulhu da ‘yan bindigar da ke haddasa ta’addanci a Jihar Zamfara ba.

A ranar Laraba, gwamnan ya halarci wani gangami da matasan Zamfara suka shirya mai taken ‘Tafiyar Zaman Lafiya’.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa, wata gamayyar matasan Zamfara sun shirya tattaki domin samar da zaman lafiya da haɗin kai, domin murnar zagayowar Ranar Dimokuraɗiyya.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa, an fara wannan gangami ne daga gidan gwamnatin jijar, wanda kuma aka ƙare a dandalin Freedom, inda dubban mutane suka taru domin nuna goyon bayansu ga gwamnati a yaƙin da take yi da ’yan bindiga.

zamfara

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Da yake gabatar da jawabinsa, Gwamna Lawal ya bayyana cewa a shirye yake ya yi duk wata yiwuwa domin ganin an dawo da zaman lafiya a dukkan sassan Jihar Zamfara.

“Ina so in gode wa ƙungiyar haɗin gwiwar matasa da suka shirya irin wannan muhimmin ‘tattakin zaman lafiya’ saboda muna buƙatar irin wannan shiri a wannan mawuyacin lokaci.

“Muna da dogon tarihi na kasancewa mutane da jiha masu zaman lafiya. Duk da haka, a cikin ‘yan shekaru, abubuwa sun canja sosai. Wannan yana buƙatar nazari don ganin inda muka yi kuskure da yin gyare-gyaren da suka dace. Tsaro alhakin kowa ne; dole ne mu bada haɗin kai da goyon bayan tsarin.

zamfara

“A koyaushe ina maimaita cewa; babu wani abu wai shi “sulhu” da ‘yan ta’adda, mun ga yadda gwamnatocin baya suka yi yunƙurin sasantawa, wanda hakan ya ƙara wa ’yan bindiga ƙwarin gwiwa.

“A wannan ranar dimokuraɗiyya, kuma da bukukuwan Sallah, ina mai farin cikin sanar da cewa na amince da biyan albashin watan Yuni ga ma’aikatan jihar Zamfara, baya ga albashin, mun cika alƙawarin da muka ɗauka na aiwatar da mafi ƙarancin albashin Naira dubu 30, saɓanin yadda aka saba da dubu bakwai.

“Zan ci gaba da aiki don ci gaban jihar mu da kuma tallafa wa mutanen mu. Mun samu ci gaba sosai a fannin tsaro, ilimi, noma, kiwon lafiya, samar da ababen more rayuwa da ƙarfafawa da dai sauransu.

  • ‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano

 

“Da wannan zaman lafiya, mun aike da saƙo mai ƙarfi ga maƙiya jihar cewa mun haɗa kai a matsayin mu na al’umma, kuma gwamnati ta jajirce wajen ganin ta kawo ƙarshen matsalar ’yan bindiga a Jihar Zamfara.

zamfara
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
Labarai

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Next Post
Ba Za A Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gaza Ba Har Sai Amurka Ta Daina Samarwa Isra’ila Da Makamai

Ba Za A Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gaza Ba Har Sai Amurka Ta Daina Samarwa Isra’ila Da Makamai

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.