ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da ‘Tattakin Zaman Lafiya’ A Jihar Zamfara

Gwamna Dauda Ya Jaddada Cewa Babu Sulhu Da 'Yan Bindiga

by Leadership Hausa
2 years ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya sake jaddada cewa gwamnatin sa ba za ta taɓa shiga sulhu da ‘yan bindigar da ke haddasa ta’addanci a Jihar Zamfara ba.

A ranar Laraba, gwamnan ya halarci wani gangami da matasan Zamfara suka shirya mai taken ‘Tafiyar Zaman Lafiya’.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa, wata gamayyar matasan Zamfara sun shirya tattaki domin samar da zaman lafiya da haɗin kai, domin murnar zagayowar Ranar Dimokuraɗiyya.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa, an fara wannan gangami ne daga gidan gwamnatin jijar, wanda kuma aka ƙare a dandalin Freedom, inda dubban mutane suka taru domin nuna goyon bayansu ga gwamnati a yaƙin da take yi da ’yan bindiga.

zamfara

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Da yake gabatar da jawabinsa, Gwamna Lawal ya bayyana cewa a shirye yake ya yi duk wata yiwuwa domin ganin an dawo da zaman lafiya a dukkan sassan Jihar Zamfara.

“Ina so in gode wa ƙungiyar haɗin gwiwar matasa da suka shirya irin wannan muhimmin ‘tattakin zaman lafiya’ saboda muna buƙatar irin wannan shiri a wannan mawuyacin lokaci.

“Muna da dogon tarihi na kasancewa mutane da jiha masu zaman lafiya. Duk da haka, a cikin ‘yan shekaru, abubuwa sun canja sosai. Wannan yana buƙatar nazari don ganin inda muka yi kuskure da yin gyare-gyaren da suka dace. Tsaro alhakin kowa ne; dole ne mu bada haɗin kai da goyon bayan tsarin.

zamfara

“A koyaushe ina maimaita cewa; babu wani abu wai shi “sulhu” da ‘yan ta’adda, mun ga yadda gwamnatocin baya suka yi yunƙurin sasantawa, wanda hakan ya ƙara wa ’yan bindiga ƙwarin gwiwa.

“A wannan ranar dimokuraɗiyya, kuma da bukukuwan Sallah, ina mai farin cikin sanar da cewa na amince da biyan albashin watan Yuni ga ma’aikatan jihar Zamfara, baya ga albashin, mun cika alƙawarin da muka ɗauka na aiwatar da mafi ƙarancin albashin Naira dubu 30, saɓanin yadda aka saba da dubu bakwai.

“Zan ci gaba da aiki don ci gaban jihar mu da kuma tallafa wa mutanen mu. Mun samu ci gaba sosai a fannin tsaro, ilimi, noma, kiwon lafiya, samar da ababen more rayuwa da ƙarfafawa da dai sauransu.

  • ‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano

 

“Da wannan zaman lafiya, mun aike da saƙo mai ƙarfi ga maƙiya jihar cewa mun haɗa kai a matsayin mu na al’umma, kuma gwamnati ta jajirce wajen ganin ta kawo ƙarshen matsalar ’yan bindiga a Jihar Zamfara.

zamfara
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Ba Za A Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gaza Ba Har Sai Amurka Ta Daina Samarwa Isra’ila Da Makamai

Ba Za A Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gaza Ba Har Sai Amurka Ta Daina Samarwa Isra’ila Da Makamai

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.