Mai magana da yawun ofishin lura da batun yankin Taiwan a majalisar gudanarwar kasar Sin Zhu Fenglian, ta jaddada adawar kasar Sin ga tsoma bakin duk wani sashe na waje cikin batun yankin Taiwan. Zhu ta furta hakan ne yayin da take mayar da martani, ga shirin jagoran Taiwan Lai Ching-te na sayen makamai daga Amurka.
Zhu ta ce “Muna da karfin iko, da kwarin gwiwa, da aniya, da damar murkushe duk wani dan a-ware dake neman ‘’yancin kan Taiwan’, kuma dunkulewar sassan kasar Sin waje guda, abu ne da ba za a iya dakatar da shi ba.
Dan gane da tambayar da aka yi mata, game da takardun manufar tsaron kasa da Amurka ta fitar, wadanda a cikinsu Amurkan ta ce ba ta goyon bayan duk wasu sauye-sauye daga bangare guda, a tabbataccen matsayin zirin Taiwan, Zhu ta ce tabbataccen matsayin zirin Taiwan shi ne kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma dukkanin bangarori biyu na zirin Taiwan na karkashin kasar Sin daya tak.
Daga nan sai ta yi kira ga Amurka da ta yi taka-tsantsan da batun Taiwan, tana mai gargadinta da kada ta bari wasu tsirarrun ’yan a-ware masu rajin neman “’yancin kan Taiwan”, su jefa Sin da Amurka cikin yanayi mai hadari na tashin hankali da fito-na-fito. (Saminu Alhassan)














