Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa, sabon babi na zaman lafiya da sulhu ya fara aiki, wanda hakan ke nuna an kawo karshen watanni na rashin jituwa a tsakanin mambobinta.
Majalisar Amintattun Jam’iyyar (BoT) ce ta bayyana hakan, tana mai alkawarin cewa, ta bayar da cikakken goyon bayanta ga Kwamitin Aiki na Kasa (NWC) wanda Kabiru Tanimu Turaki, SAN, ya jagoranta kwanan nan.
A wani taro da manyan jiga-jigan jam’iyyar suka halarta, ciki har da tsohon Ministan Yada Labarai, Farfesa Jerry Gana; tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Ahmed Muhammed Makarfi, da tsohon gwamnan Jihar Enugu, Dr. Okwesilieze Nwodo, kuma Shugaban BoT, Sanata Adolphus Wabara, sun jaddada muhimmancin karfafa hadin kan ‘ya’yan jam’iyyar.
“Da farko, bari in taya PDP murna kan nasarar gudanar da Babban Taron Kasa a Ibadan, Jihar Oyo. Babban Taron ya nuna jajircewar Jam’iyyarmu ga dimokuradiyya da gaskiya,” in ji Wabara.














