Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya ziyarci Hadaddiyar Daular Larabawa, da Saudiyya, da kuma Jordan daga ranar 12 zuwa 16 ga watan nan, inda bayan ziyarar ya zanta da manema labarai na kasar Sin.
Game da batun Taiwan, Wang Yi ya furta cewa, yayin ziyarar tasa, ya bayyana wa kasashen uku hakikanin abun da ya auku a tarihi, da dokokin da batun Taiwan ya shafa, tare da nuna kiyayya mai karfi game da danyen aiki da shugabanni masu ci na kasar Japan suka yi, na sanya hannu cikin harkokin cikin gidan kasar Sin.
A nasu bangaren, kasashen uku sun nanata mutunta manufar “Kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”, da mara baya ga kasar Sin kan kiyaye ikon mulkinta, da cikakkun yakunanta, da kuma burinta na dinke sassan kasa da kasa guri daya. An taba yi wa al’ummun kasashen Larabawa mulkin mallaka, kamar yadda aka taba yi wa al’ummun Sin mamaya, don haka suna iya fahimtar kasar Sin sosai. Wang ya ce, yadda kasashen Larabawa ke goyon bayan matsayin Sin kan batun Taiwan, mutuntawa ne ga ka’idojin dangantakar kasa da kasa, wanda ya shaida amincewar sassan kasa da kasa ga manufar “Kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”.
Ban da wannan kuma, Wang Yi ya nuna cewa, a bana ake cika shekaru 80 da samun nasarar yakin turjiyar jama’ar kasar Sin kan zaluncin Japanawa, da kuma yakin duniya na biyu. A da, masu nuna karfin soja na Japan sun yi kiri-da-muzu, sun kai wa wasu kasashe hare-hare bisa hujjar wai “Japan na fuskantar barazanar dorewa”, don haka dole ne a magance sake aukuwar wannan mummunan lamari a zamanin yau.
A wata sabuwa kuma, Wang Yi ya tattauna da takwaransa na kasar Masar Badr Abdelatty ta wayar tarho, a jiya Talata 16 ga wata, inda Abdelatty ya bayyana cewa, kasarsa na jinjinawa muhimmin ra’ayin da kasar Sin ta gabatar na warware batun Falasdinu, da kuma sabon tallafi da ta samar wanda za ta bai wa Falasdinu. Kana Masar na goyon bayan muhimmiyar rawar da Sin ke takawa, a ayyukan maido da zaman lafiya da sake gina zirin Gaza.
Game da hakan, Wang Yi ya furta cewa, Sin za ta ci gaba da goyon bayan Masar, a fannin ba da gudummawar a-zo-a-gani, ga aikin kiyaye zaman lafiya a shiyyoyi. (Kande Gao)














