Gwamnatin jihar Borno ta musanta zarge-zargen cewa an biya kudin fansa domin kubutar da mutane 360 da aka ceto daga tsaunukan Mandara, wanda ya yi fice a matsayin maɓoyar ’yan ta’adda a kudancin jihar.
Kwamishinan yada labarai da harkokin tsaron cikin gida na jihar, Usman Tar, ne ya karyata zargin yayin wata hira da ya yi a shirin ‘The Morning Brief’ na gidan talabijin na Channels ranar Litinin, inda ya ce an kuɓutar da mutanen ne ta hanyar hadin gwiwar aikin soja tare da taimakon bayanan sirri.
Kalaman nasa sun biyo bayan sanarwar da Operation Hadin Kai (OPHK) ta fitar ranar Lahadi cewa dakarunta sun samu nasarar ceto wadanda aka sace daga sansanin kungiyar Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal-Jihad (JAS) bayan makonni na leken asiri.
A cikin wata sanarwa, mukaddashin jami’in yada labarai na OPHK, Laftanar Kanar Haruna Sani, ya ce dakarun musamman da sojojin shiyya 1 ne suka gudanar da aikin bayan tattara bayanan sirri da binciken sirri na musamman.
A cewar rundunar sojin, mutanen da aka ceto — maza, mata da yara — an tsare su cikin mawuyacin hali bayan an sace su daga kauyuka da dama, musamman a yankin Ngoshe.
Da yake mayar da martani kan zargin cewa an biya kudin fansa domin a sake su, Tar ya musanta hakan sosai tare da kalubalantar masu wannan ikirari da su gabatar da hujja.















Discussion about this post