Kasar Sin ta ce kofarta a bude take, domin warware takaddamar cinikayya tsakaninta da kungiyar Tarayyar Turai (EU) cikin kyakkyawar zuciya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian ne ya bayyana haka, yau Litinin lokacin da yake amsa tambayoyi yayin taron manema labarai na yau da kullum, inda ya ce Sin na fatan EU za ta hada hannu da ita wajen lalubo mafita ta hanyar tattaunawa da tuntubar juna da kuma tabbatar da hadin gwiwar cinikayya da tattalin arziki a tsakaninsu, ta amfani harkokin kasuwanci da jama’ar bangarorin biyu. A wani labarin kuma, a ranekun 11 da 12 ga watan Yuni, za a yi taron manyan jami’ai na 2026 kan tafiyar da harkokin da suka shafi hakkokin dan Adam a birnin Beijing, albarkacin cika shekaru 40 da amincewa da Sanarwar MDD kan Hakkin Ci Gaba, da kuma nemo hanyoyin tabbatar da kare hakkokin dan Adam.
Da yake amsa tambaya game da batun, Lin Jian ya ce taron zai samu mahalarta sama da 400 da suka hada da Sinawa da baki daga kasashe kusan 100, haka kuma an gayyaci MDD da sauran hukumomin kasa da kasa da na shiyya shiyya.
Ya ce Sin na fatan dukkan bangarori za su musaya tare da koyo daga juna da cimma matsaya kan batun inganta kare hakkokin dan Adam ta hanyar samar da ci gaba, da kuma hada hannu wajen cimma kyakkyawan burin Sanarwa Kan Hakkin Ci Gaba, domin gina tsarin tafiyar da hakkokin dan Adam cikin adalci da sanin ya kamata da tafiya tare da kowa. (Fa’iza Mustapha)














Discussion about this post