Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian, ya shugabanci wani taron manema labarai a yau Litinin 20 ga watan nan, inda aka tambaye shi cewa, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya bayyana cewa, har yanzu ana shirye-shiryen ziyarar shugaba Xi Jinping a Amurka a watan Satumban bana.
Shin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ita ma tana ganin ana shirye-shiryen haka? Lin Jian ya ba da amsar cewa, diflomasiyya ta bangaren shugabanni na da matukar muhimmanci ga dangantakar Sin da Amurka, kuma har yanzu bangarorin biyu suna tuntubar juna game da batun inganta mu’amalar shugabanninsu a bana.
Kazalika, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya sanar da cewa, memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, wanda kuma shi ne ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi, zai halarci taron ministocin harkokin wajen kasar Sin da kasashen kungiyar ASEAN wanda zai gudana a ranar 22 ga watan Yuli a birnin Manila na kasar Philippines, kana, zai halarci taron majalisar ministocin harkokin wajen kasashe membobin kungiyar hadin kai ta Shanghai wato SCO a takaice a garin Cholpon-Ata na kasar Kyrgyzstan tare kuma da ziyartar kasar daga ranar 23 zuwa 25 ga watan nan. (Murtala Zhang)














