• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Gombe Na Bai Wa Fannin Noman Auduga  Mahimmanci – Kwamishina

by Abubakar Abba
2 years ago
Gombe

Gwamnatin  jihar Gombe ta bayyana cewa, ta na bai wa harkar noman Auduga muhimmanci, musamman domin ta kara bunkasa fannin a daukacin fadin jihar, samar da ayyukan yi ga ‘yan jihar,  kara habaka tattalin arzikin jihar da kuma kara bai wa manomanta kwarin guiwa.

Furuncin hakan ya fito ne daga bakin Kwamishinan Aikin Gona na Jihar, Muhammad Magaji Gettado a jawabinsa a lokacin want taro da aka gudanar a kwanan baya a jihar akan yadda za a kara bunkasa fannin, musamman a jihar.

  • Takaddamar Da Ta Kunno Kai Lokacin Tantance Ministocin Tinubu
  • Gwamna Dauda Ya Karbi ‘Yan Mata Hudu Da Suka Kwashe Watanin 7 A Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

A cewarsa, a baya manoman na Audugar a jihar sun funaci matsaloli, inda ya bayyana cewa, amma tuni gwamnatin jihar ta magance wadanan natsalolin, musamman ganin yadda ta samar wa manomanta kayan aikin noma na zamani da sauransu

Magaji ya kara da cewa, akwai kuma bukatar a ilimantar da manomata, musaman wajen samar masu da ingantacce Iri wanda hakan zai taimaka masu don su kara bunkasa noman na su na Audgar a jihar.

A cewarsa,”Gwamnatin Jihar ta na bai wa harkar noman auduga muhimmanci kasancewar ta fanni ne da ke kara bunkasa tattalin arziki. “

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Shi kuwa a na sa jawabin a matsayin babban bako a wajen taron shugaban kungiyar manoman Auduga na kasa Alhaji Lawan Sani Matazu, ya bayyana cewa, a watannin da suka gabata, kungiyar ta kaddamar da shirin  habaka noman Auduga a jihar, wanda ya ce, waccan kaddamar kwaliya ta but ya kudin Subulu, musamman ganin cewa, fannin na kara bunkasa a jihar.

A cewarsa, jihar ta Gombe  kusan a daukacin fadin kasar nan, ita ce ke a gaba wajen noman auduga, inda ya yi kira ga gwamnatin jihar da ci gaba da bai wa fannin mahimmanci domin jihar ta ci gaba da rike wannan kambun na ta.

” A watannin da suka gabata, kungiyar ta kaddamar da shirin  habaka noman Auduga a jihar, wanda ya ce, waccan kaddamar kwaliya ta but ya kudin Subulu, musamman ganin cewa, fannin na kara bunkasa a jihar.  “

Matazu, ya ce noman Auduga hanyar ci gaba ne ga matasa domin, fannin na samar da aikin yi da kuma kudin  shiga, musamman ga manoman da suka rungumi fannin ka’in da na’in.

Ya  buga misali da cewa, ingantacce Irin nomanta da Babban Bankin Nijeriya CBN, ya rabarwar da wasu manomanta ‘ya’yan kungiyar a jihar ta Gombe, hakan ya kara taimaka wa wajen kara bunkasa nomanta a jihar da kuma kasa baki daya.

“Ingantacce Irin nomanta da Babban Bankin Nijeriya CBN, ya rabarwar da wasu manomanta ‘ya’yan kungiyar a jihar ta Gombe, hakan ya kara taimaka wa wajen kara bunkasa nomanta a jihar da kuma kasa baki daya. “

Kazalika ya bayyana cewa,bashin, da bankin ya bai wa manomanta a jihar shi ma ya taimaka wajen bunkasa sana’ar su da kara samar wa da kansu da kudaden shiga.

Shugaban ya kuma yi kira ga manomanta da su tabbatar da suna shuka ingantacce irin na Audugar domin su dinga samun dimbin kudaden shiga da kuma samun amfani mai yawa idan sun yi girbi.

” Ina kira ga manomanta da su tabbatar da suna shuka ingantacce irin na Audugar domin su dinga samun dimbin kudaden shiga da kuma samun amfani mai yawa idan sun yi girbi. “

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Next Post
Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 122 A Nijeriya -UNICEF

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 122 A Nijeriya -UNICEF

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.