ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Da Ta Kunno Kai Lokacin Tantance Ministocin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

A wannan makon ne majalisa ta fara tantance mutanen da Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya kake mata domin nada su mukaman ministoci.

Tun farko, shugaban kasa ya aika wa majalisa sunayen mutum 28 domin a tantance su, inda za su gurfana a gaban ‘yan majalisa domin amsa tambayoyi, sai dai kuma wasu daga ciki ‘yan majalisan ba su tsaurara tambayoyin ba, yayin da wasu kuma suka sha tambayoyi masu yawa. A yayin tantance ministocin, an samu takaddama a zauren majalisa har sai da aka bukaci wasu su kawo wa majalisa takardun haifuwa da shaidar takardun makarantarsu.

  • An Fara Taron Harkokin Sufurin Jiragen Sama Ta 2023 A HK
  • Kaska Za ta Mutu Da Haushin Kifi

A ranar Alhamis da ta gabata ne Majalisar Dattawa ta fitar da jerin sunayen wadanda Tinubu zai nada mukamin ministoci da zai kafa majalisar zartarwarsa, inda majalisa za ta tantance su kafin a tabbatar da nadin nasu.

ADVERTISEMENT

Tinubu dai ya cika wa’adin watanni biyu da kundin tsarin mulkin kasar ya ba shi da dukkan gwamnonin su gabatar da jerin sunayen wadanda za su nada ga majalisar domin a tantance su a zauren majalisar.

Sunayen sun hada da tsoffin gwamnoni hudu, mata bakwai, ‘yan majalisa tsoffi da sababbi, an zabo su ne daga jihohi 25 cikin 36 na Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

Tsarin mulkin kasar nan ya bai wa shugaban kasa damar zabo akalla minista daga kowace jiha, ana sa ran Tinubu zai mika wa majalisa karin sunayen mutane 11 a cikin kwanaki masu zuwa.

Tsofaffin gwamnonin guda hudu sun hada da Dabid Umahi, Nyesom Wike, Nasiru El-Rufai da kuma Abubakar Badaru.

Sauran sun hada da Abubakar Momoh, Ambassador Yusuf Miatama Tukur, Arch. Ahmed Dangiwa, Cif Uche Nnaji, Rt. Hon. Ekperipe Ekpo, Hon. Olubunmi Tunji Ojo, Mista Bello Muhammad G, Mista Dele Alake, Mista Lateef Fagbemi SAN, Mis-ta Muhammad Idris, Mista Olawale Edun, Mista Waheed Adebayo Adelabu, Farfe-sa Ali Pate, Professor Joseph Utseb, Sanata Abubakar Kyari, Sanata John Eno, da kuma Sanata Sani Abubakar Danladi.

A cikin wasikar da Tinubu ya aika wa majalisa, ya ce sunayen mutane 28 ne kashin farko na jerin sunayen ministocin da yake son nadawa, kuma ya yi alkawarin tura sauran nan da wani lokaci mai zuwa.

Sai dai wasu ‘yan Nijeriya sun bayyana shakku a kan yadda tsoffin ‘yan majalisa suke kubuta daga tambayoyin ‘yan majalisa.

‘Yan Nijeriya na sa ran ‘yan majalisun za su gudanar da aikin tantancewar ta han-yar da ta dace da abin da jama’a ke bukata.

An dai samu ce-ce-ku-ce a zauren majalisa a wurin tantance sunayen ministocin Shugaba Tinubu a lokacin da Farfesa Joseph Terlumun Utseb, wanda aka zaba daga Jihar Benuwai, ya ce ya fara karatun firamare tun yana dan shekara hudu.

Tun da farko yayin da yake gabatar da kansa, ya yi ikirarin an haife shi a 1980 kuma ya fara makarantar firamare a 1984.

Farfesa Utseb ya dage cewa an haife shi ne a shekarar 1980 kuma ya fara karatun firamare a shekarar 1984, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a zauren majalisar dattawa.

Duk da haka, bayan amsa tambayoyi kan abin da zai yi idan aka nada Ministan Al-barkatun Ruwa ta ya ya zai shawo kan ambaliyar ruwa a kasar, inda daga bisani aka bukaci Utseb ya tafi.

Shi ma Olubunmi Tunji-Ojo wanda shi dan majalisar wakilai ne ya bayyana cewa an haife shi a shekara ta 1982.

Ya dai kammala karatunsa ne a shekara ta 2005 daga jami’ar kasar Ingila, sannan ya yi bautar kasa a shekarar 2020 yana dan shekara 38 a lokacin da ya taba zama dan majalisar wakilai.

Yin bautar kasa ya kasance ne ga wadanda ke da shekaru kasa da 30.

Ojo ya bayyana cewa yana da shekaru 28 a lokacin da ya kammala karatunsa na jami’a, amma ya ci gaba da zama a kasar Ingila.

Ya yi nuni da cewa doka ta goyi bayan ya yi bautar kasa yana da shekaru 38 bayan ya dawo kasar nan.

Shi kuwa wanda aka zaba daga Jihar Taraba, Mohammed Danlandi ya sha am-bayoyi a lokacin tantancewa. An zarge shi da cewa kotun koli ta hana shi rike mukamin siyasa na tsawon shekaru 10.

Danlandi ya musanta wannan ikirarin, ya kara da cewa a halin yanzu lamarin yana gaban kotun koli.

Daga nan ne aka bukaci ya wuce a matsayinsa na tsohon dan majalisar dattawa.

Bayan haka, wanda aka zaba daga Jihar Sakkwato, Bello Mohammed, ya samu matsala a takardun karatunsa na kammala sakandare, inda a ciki aka samu darasi biyu kacal ya ji kuma ya samu gurbin shiga jami’a.

Wani dan majalisa ya so sanin yadda ya samu shiga jami’a ba tare da ya samu cin darashi biyar kamar yadda doka ta tanada.

Sai dai Bello ya ce abin da kundin tsarin mulki ya tanada shi ne, takardar shaidar kammala sakandare don tsayawa takara ba ta bukatar sai an ci darasi biyar ciki har da lissafi da turanci.

Ya ce ya yi wasu jarrabawar shaidar kammala makaranta da ya ba shi damar samun gurbin shiga jami’a. Sai dai bai bayar da sakamakon sauran jarrabawar da ya yi ga majalisar dattawa ba.

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya bukace shi da ya aika da wadannan takaddun zuwa zauren majalisar dattawa.

‘Yan majalisar sun gasa wa Betta Edu, Uju Ohaneye da Misis Imaan Sulaiman Ibra-him aya a hannu wajen tambayoyi har na kusan minti 30 kowanne su.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Manyan Labarai

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya
Manyan Labarai

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Next Post
Ronaldo Ya Jefa Kwallon Da Ta Saka Kungiyarsa Zagayen Gaba A Gasar Zakarun Larabawa

Ronaldo Ya Jefa Kwallon Da Ta Saka Kungiyarsa Zagayen Gaba A Gasar Zakarun Larabawa

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.