Mataimakin firaministan Sin Liu Guozhong, ya yi rangadi a birnin Beijing a yau Lahadi, inda ya jaddada wajibcin nazari da aiwatar da umarnin shugaba Xi Jinping da na taron majalisar gudanarwar kasar dangane da matakan tunkarar guguwar ruwan sama da kandagarkin ambaliya.
Ya kuma kara da yin kira da kada a yi kasa a gwiwa wajen gudanar da ingantaccen aikin kare ma’adanan ruwa a lokacin da ake samun ambaliya, ta yadda za a bayar da ingantaccen tabbacin kare rayukan jama’a da dukiyoyinsu. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
ADVERTISEMENT














