ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Zamfara Saniyar Ware Wajen Tallafin Kuɗi Saboda Ba Ta APC – Dauda Lawal

by Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa jihar sa ba ta taba samun wani kuɗin tallafi daga Gwamnatin Tarayya ba tun bayan hawan sa mulki a shekarar 2023.

 

Ya bayyana haka ne a lokacin da gwamnoni ke tururuwar komawa APC mai mulki domin samun tagomashin Gwamnatin Tarayya.

ADVERTISEMENT
  • Dokar Zaɓe: An Harba Barkonon Tsohuwa Ga Masu Zanga-zanga A Majalisa
  • Dokar Zaɓe: An Harba Barkonon Tsohuwa Ga Masu Zanga-zanga A Majalisa

Da yake zantawa da kafar yaɗa labarai ta DW Hausa, gwamnan PDP ɗin, ya ce akwai jihohi da suka samu maƙudan kuɗi daga Gwamnatin Tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa Zamfara ba ta samu ko sisi ba face kuɗin da doka ta tanada.

 

A cewar sa, “Gwamnatin Tarayya ba ta taba ba mu wani kuɗin tallafi ba kamar yadda ta yi wa wasu jihohi. Ina da sahihin bayani cewa wasu jihohi sun samu sama da Naira biliyan 500, amma jihata ba ta samu ko kobo ɗaya ba.”

 

Ya ƙara da cewa, yana ganin hakan na da alaƙa da kasancewar sa a jam’iyyar adawa, inda ya bayyana cewa, “Ina ganin hakan ne saboda ba mu jam’iyya ɗaya da su ba. Ni ina jam’iyyar adawa.”

 

Rahotanni sun nuna cewa Gwamna Dauda Lawal ne kaɗai gwamna daga jam’iyyar adawa a yankin Arewa maso Yamma, yayin da sauran jihohin yankin ke ƙarƙashin APC.

 

Duk da haka, ya jaddada cewa rashin ƙarin tallafi daga tarayya bai hana gwamnatin sa aiwatar da ayyukan raya ƙasa ba.

 

Ya ce, “tun bayan da ya zama gwamna a 2023, ba su samu wani ƙarin tallafi daga gwamnatin tarayya ba baya ga abin da doka ta ware.

 

Gwamna Lawal ya kuma bayyana cewa gwamnatinsa ba ta karbi wani sabon bashi domin tafiyar da harkokin jihar ba, duk da ƙalubalen da ake fuskanta.

 

Ya ce, wannan na da alaƙa da bashin da gwamnatin da ta gabata ta karba, wanda har yanzu ake biya.

 

Game da makomarsa ta siyasa, gwamnan ya ce ba zai sauya sheƙa daga PDP nan take ba duk da matsalolin cikin gida da jam’iyyar ke fuskanta.

 

Kamar dai yadda muka sani, Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da a biya albashi da kuɗin fansho na watan Fabrairu cikin gaggawa kafin fara azumin watan Ramadan.

 

Rahotanni sun bayyana cewa gwamnan ya bayar da umarni ga Akanta Janar na jihar da ya saki kuɗin ba tare da bata lokaci ba domin ma’aikata da masu karbar fansho su samu sauƙin shirin azumi.

 

Wannan mataki na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da al’adu na jihar, Mahmud Dantawasa, ya sanya wa hannu a ranar Litinin, 16 ga watan Fabrairun 2026.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

SAHUR [Falalarsa Da Fa'idojinsa] Na 1

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.