ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Zamfara Saniyar Ware Wajen Tallafin Kuɗi Saboda Ba Ta APC – Dauda Lawal

by Sulaiman
4 months ago
Zamfara

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa jihar sa ba ta taba samun wani kuɗin tallafi daga Gwamnatin Tarayya ba tun bayan hawan sa mulki a shekarar 2023.

 

Ya bayyana haka ne a lokacin da gwamnoni ke tururuwar komawa APC mai mulki domin samun tagomashin Gwamnatin Tarayya.

ADVERTISEMENT
  • Dokar Zaɓe: An Harba Barkonon Tsohuwa Ga Masu Zanga-zanga A Majalisa
  • Dokar Zaɓe: An Harba Barkonon Tsohuwa Ga Masu Zanga-zanga A Majalisa

Da yake zantawa da kafar yaɗa labarai ta DW Hausa, gwamnan PDP ɗin, ya ce akwai jihohi da suka samu maƙudan kuɗi daga Gwamnatin Tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa Zamfara ba ta samu ko sisi ba face kuɗin da doka ta tanada.

 

A cewar sa, “Gwamnatin Tarayya ba ta taba ba mu wani kuɗin tallafi ba kamar yadda ta yi wa wasu jihohi. Ina da sahihin bayani cewa wasu jihohi sun samu sama da Naira biliyan 500, amma jihata ba ta samu ko kobo ɗaya ba.”

 

Ya ƙara da cewa, yana ganin hakan na da alaƙa da kasancewar sa a jam’iyyar adawa, inda ya bayyana cewa, “Ina ganin hakan ne saboda ba mu jam’iyya ɗaya da su ba. Ni ina jam’iyyar adawa.”

 

Rahotanni sun nuna cewa Gwamna Dauda Lawal ne kaɗai gwamna daga jam’iyyar adawa a yankin Arewa maso Yamma, yayin da sauran jihohin yankin ke ƙarƙashin APC.

 

Duk da haka, ya jaddada cewa rashin ƙarin tallafi daga tarayya bai hana gwamnatin sa aiwatar da ayyukan raya ƙasa ba.

 

Ya ce, “tun bayan da ya zama gwamna a 2023, ba su samu wani ƙarin tallafi daga gwamnatin tarayya ba baya ga abin da doka ta ware.

 

Gwamna Lawal ya kuma bayyana cewa gwamnatinsa ba ta karbi wani sabon bashi domin tafiyar da harkokin jihar ba, duk da ƙalubalen da ake fuskanta.

 

Ya ce, wannan na da alaƙa da bashin da gwamnatin da ta gabata ta karba, wanda har yanzu ake biya.

 

Game da makomarsa ta siyasa, gwamnan ya ce ba zai sauya sheƙa daga PDP nan take ba duk da matsalolin cikin gida da jam’iyyar ke fuskanta.

 

Kamar dai yadda muka sani, Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da a biya albashi da kuɗin fansho na watan Fabrairu cikin gaggawa kafin fara azumin watan Ramadan.

 

Rahotanni sun bayyana cewa gwamnan ya bayar da umarni ga Akanta Janar na jihar da ya saki kuɗin ba tare da bata lokaci ba domin ma’aikata da masu karbar fansho su samu sauƙin shirin azumi.

 

Wannan mataki na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da al’adu na jihar, Mahmud Dantawasa, ya sanya wa hannu a ranar Litinin, 16 ga watan Fabrairun 2026.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

MASU ALAKA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

SAHUR [Falalarsa Da Fa'idojinsa] Na 1

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.