ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Zamfara Saniyar Ware Wajen Tallafin Kuɗi Saboda Ba Ta APC – Dauda Lawal

by Sulaiman
7 months ago
Zamfara

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa jihar sa ba ta taba samun wani kuɗin tallafi daga Gwamnatin Tarayya ba tun bayan hawan sa mulki a shekarar 2023.

 

Ya bayyana haka ne a lokacin da gwamnoni ke tururuwar komawa APC mai mulki domin samun tagomashin Gwamnatin Tarayya.

ADVERTISEMENT
  • Dokar Zaɓe: An Harba Barkonon Tsohuwa Ga Masu Zanga-zanga A Majalisa
  • Dokar Zaɓe: An Harba Barkonon Tsohuwa Ga Masu Zanga-zanga A Majalisa

Da yake zantawa da kafar yaɗa labarai ta DW Hausa, gwamnan PDP ɗin, ya ce akwai jihohi da suka samu maƙudan kuɗi daga Gwamnatin Tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa Zamfara ba ta samu ko sisi ba face kuɗin da doka ta tanada.

 

A cewar sa, “Gwamnatin Tarayya ba ta taba ba mu wani kuɗin tallafi ba kamar yadda ta yi wa wasu jihohi. Ina da sahihin bayani cewa wasu jihohi sun samu sama da Naira biliyan 500, amma jihata ba ta samu ko kobo ɗaya ba.”

 

Ya ƙara da cewa, yana ganin hakan na da alaƙa da kasancewar sa a jam’iyyar adawa, inda ya bayyana cewa, “Ina ganin hakan ne saboda ba mu jam’iyya ɗaya da su ba. Ni ina jam’iyyar adawa.”

 

Rahotanni sun nuna cewa Gwamna Dauda Lawal ne kaɗai gwamna daga jam’iyyar adawa a yankin Arewa maso Yamma, yayin da sauran jihohin yankin ke ƙarƙashin APC.

 

Duk da haka, ya jaddada cewa rashin ƙarin tallafi daga tarayya bai hana gwamnatin sa aiwatar da ayyukan raya ƙasa ba.

 

Ya ce, “tun bayan da ya zama gwamna a 2023, ba su samu wani ƙarin tallafi daga gwamnatin tarayya ba baya ga abin da doka ta ware.

 

Gwamna Lawal ya kuma bayyana cewa gwamnatinsa ba ta karbi wani sabon bashi domin tafiyar da harkokin jihar ba, duk da ƙalubalen da ake fuskanta.

 

Ya ce, wannan na da alaƙa da bashin da gwamnatin da ta gabata ta karba, wanda har yanzu ake biya.

 

Game da makomarsa ta siyasa, gwamnan ya ce ba zai sauya sheƙa daga PDP nan take ba duk da matsalolin cikin gida da jam’iyyar ke fuskanta.

 

Kamar dai yadda muka sani, Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da a biya albashi da kuɗin fansho na watan Fabrairu cikin gaggawa kafin fara azumin watan Ramadan.

 

Rahotanni sun bayyana cewa gwamnan ya bayar da umarni ga Akanta Janar na jihar da ya saki kuɗin ba tare da bata lokaci ba domin ma’aikata da masu karbar fansho su samu sauƙin shirin azumi.

 

Wannan mataki na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da al’adu na jihar, Mahmud Dantawasa, ya sanya wa hannu a ranar Litinin, 16 ga watan Fabrairun 2026.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

SAHUR [Falalarsa Da Fa'idojinsa] Na 1

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.