Rundunar ‘yansandan Nijeriya na fuskantar suka daga ɓangarori daban-daban bayan zargin jami’anta da harba barkonon tsohuwa ga masu zanga-zangar da suka mamaye Majalisar Dokoki ta Kasa a ranar Talata, suna kalubalantar tsarin tura sakamakon zabe ta hanyar intanet, inda suka ce dole a saka kalmar (real-time) a cikin Dokar Kwaskwarima ta Dokar Zabe ta 2026.
Masu zanga-zangar, wadanda suka koma Majalisar Dokoki ta Kasa bayan hutun kwanaki biyar, sun dakatar da zanga-zangarsu a baya bayan da aka basu tabbacin yin gyara a zaman da aka yi ranar Talatar makon da ya gabata.
In za a iya tuna cewa, Majalisar Dattawa ta yi zaman gaggawa a ranar Talatar da ta gabata don sake duba shawarar da ta yanke mai cike da ce-ce-ku-ce kan Sashe na 60(3) na Dokar Kwaskwarima ta Dokar Zabe, bayan koke-koken jama’a da dama.
A lokacin zaman, Babban Mai tsawatarwa na Majalisar Dattawa, Sanata Tahir Monguno (APC, Borno ta Arewa), ya gabatar da kudiri na cire kalmar “real-time, ainihin lokaci” daga cikin sashen, yayin da kuma ya nemi maye gurbin kalmar “transmission” da “transfer” – wannan matakin ne ya jawo suka mai zafi daga kungiyoyin fararen hula da masu fafutukar kare dokar gyaran zabe.















Discussion about this post