Gwamnatin Jihar Jigawa ta fara gudanar da tantancewa ta kwamfuta (CBT) domin ɗaukar malamai 500 ƙarƙashin shirin J-Tsangaya, yayin da sama da mutane 9,000 masu digiri da masu takardar shaidar NCE suka nemi guraben aikin. Sakataren Hukumar Ilimin Tsangaya na jihar, Abubakar Maje, ya bayyana haka yayin duba cibiyoyin jarabawar da ke Dutse, da Hadejia da Gumel. Ya ce an tantance masu neman aikin 3,150 domin shiga jarabawar, daga cikinsu ne za a zabi waɗanda za su samu aikin.
Maje ya ce ɗaukar malaman na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na ƙarfafa shirin Almajiri Free Zone, wanda ke da burin shigar da sama da almajirai 5,000 cikin tsarin ilimi mai haɗe da karatun Alkur’ani, da ilimin zamani da koyon sana’o’i.
Ya bayyana cewa gurbin malaman 500 zai kasance tsakanin masu koyar da darussan zamani da waɗanda za su koyar da ilimin Alkur’ani ƙarƙashin sabon tsarin karatun Tsangaya. Gwamnatin jihar ta kuma ware manyan makarantun Tsangaya guda uku a Dutse, da Kafin Hausa da Ringim, waɗanda kowacce ke da damar ɗaukar kusan yara 1,500.
Wasu daga cikin waɗanda suka rubuta jarabawar sun yaba da yadda aka gudanar da ita, amma suka buƙaci gwamnati ta ƙara yawan guraben aikin saboda yawan masu neman aikin. Shirin na daga cikin kokarin Jigawa na rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta tare da samar musu da ilimin addini, na zamani da sana’o’in dogaro da kai.














