ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Tura Ƙarin Jami’an Tsaro Don Murƙushe Ta’addanci – Minista

by Sulaiman
8 months ago
Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da kudurinta na ƙara tsananta yaki da ta’addanci da aikata laifuka a sassa daban-daban na ƙasar, bayan jerin hare-haren da suka faru kwanan nan.

A wani taron manema labarai da aka gudanar a Radio House, Abuja, ranar Laraba 19 ga Nuwamba, 2025, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar dan Jama’a, Mohammed Idris, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ɗaga matakin sha’anin tsaro zuwa matsayi mafi girma domin kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa.

  • NDLEA Ta Kama Malami Da Matarsa ​​Da Buhunan Tabar Wiwi 360 A Kuros Riba
  • Kalaman Takaichi Masu Matukar Ban-Takaici

Ministan ya miƙa sakon ta’aziyyar Shugaban Ƙasa ga iyalai da al’ummomin da abin ya shafa, yana mai bayyana kashe babban hafsan soji, sace dalibai a Jihar Kebbi da harin da aka kai cocin Eruku a Kwara a matsayin “abu mai muni” game da barazanar da ƙasar ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

Ya ce Shugaba Tinubu ya dage tafiyarsa zuwa taron G20 a Afirka ta Kudu da wasu tarukan ƙasashen waje, domin mai da hankali kan batutuwan tsaron cikin gida. Haka kuma ya umarci rundunonin soji da ‘yan sanda su tura ƙarin jami’ai zuwa Eruku da yankin ƙaramar hukumar Ekiti ta Jihar Kwara.

Ministan ya ƙara da cewa: “Jami’an tsaronmu sun samu umarni na musamman wajen ceto daliban makarantar Kebbi da gaggawa, tare da tarwatsa duk wata hanyar sadarwa ta ‘yan ta’adda a faɗin ƙasa.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

A cewar Idris, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, na can Birnin Kebbi bisa umarnin Shugaban Ƙasa, yana ganawa da Gwamnan Jihar Kebbi, shugabannin tsaro, sarakunan gargajiya, da iyalan daliban da aka sace.

Ministan ya kuma yi watsi da ƙoƙarin da wasu ke yi na bai wa rikicin fassarar addini, yana mai cewa matsalolin tsaro a Najeriya sun shafi musulmi da kirista, da kabilu daban-daban.

“A wannan lokaci, haɗin kan ƙasa shi ne kayan aikinmu mafi ƙarfi,” in ji shi. “Dole ne mu guji ƙiyayya da rarrabuwar kawuna. Abokan gaba na gaskiya su ne ‘yan ta’adda da miyagun da ke ƙoƙarin tayar da hankalin ƙasa.”

Ya jaddada matsayin Nijeriya a matsayin ƙasa mai addinai daban-daban, inda ‘yancin bauta ke cikin kundin tsarin mulki. Ya kuma kira jama’a da su tallafa wa jami’an tsaro, yana mai tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin ganin an kubutar da ɗaliban da aka sace tare da dawo da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.

Tarayya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Ba Za A Yarda Da Farfado Da Dabi’ar Japan Ta Amfani Da Karfin Soji Ba

Ba Za A Yarda Da Farfado Da Dabi’ar Japan Ta Amfani Da Karfin Soji Ba

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.