ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Tura Ƙarin Jami’an Tsaro Don Murƙushe Ta’addanci – Minista

by Sulaiman
10 months ago
Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da kudurinta na ƙara tsananta yaki da ta’addanci da aikata laifuka a sassa daban-daban na ƙasar, bayan jerin hare-haren da suka faru kwanan nan.

A wani taron manema labarai da aka gudanar a Radio House, Abuja, ranar Laraba 19 ga Nuwamba, 2025, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar dan Jama’a, Mohammed Idris, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ɗaga matakin sha’anin tsaro zuwa matsayi mafi girma domin kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa.

  • NDLEA Ta Kama Malami Da Matarsa ​​Da Buhunan Tabar Wiwi 360 A Kuros Riba
  • Kalaman Takaichi Masu Matukar Ban-Takaici

Ministan ya miƙa sakon ta’aziyyar Shugaban Ƙasa ga iyalai da al’ummomin da abin ya shafa, yana mai bayyana kashe babban hafsan soji, sace dalibai a Jihar Kebbi da harin da aka kai cocin Eruku a Kwara a matsayin “abu mai muni” game da barazanar da ƙasar ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

Ya ce Shugaba Tinubu ya dage tafiyarsa zuwa taron G20 a Afirka ta Kudu da wasu tarukan ƙasashen waje, domin mai da hankali kan batutuwan tsaron cikin gida. Haka kuma ya umarci rundunonin soji da ‘yan sanda su tura ƙarin jami’ai zuwa Eruku da yankin ƙaramar hukumar Ekiti ta Jihar Kwara.

Ministan ya ƙara da cewa: “Jami’an tsaronmu sun samu umarni na musamman wajen ceto daliban makarantar Kebbi da gaggawa, tare da tarwatsa duk wata hanyar sadarwa ta ‘yan ta’adda a faɗin ƙasa.”

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A cewar Idris, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, na can Birnin Kebbi bisa umarnin Shugaban Ƙasa, yana ganawa da Gwamnan Jihar Kebbi, shugabannin tsaro, sarakunan gargajiya, da iyalan daliban da aka sace.

Ministan ya kuma yi watsi da ƙoƙarin da wasu ke yi na bai wa rikicin fassarar addini, yana mai cewa matsalolin tsaro a Najeriya sun shafi musulmi da kirista, da kabilu daban-daban.

“A wannan lokaci, haɗin kan ƙasa shi ne kayan aikinmu mafi ƙarfi,” in ji shi. “Dole ne mu guji ƙiyayya da rarrabuwar kawuna. Abokan gaba na gaskiya su ne ‘yan ta’adda da miyagun da ke ƙoƙarin tayar da hankalin ƙasa.”

Ya jaddada matsayin Nijeriya a matsayin ƙasa mai addinai daban-daban, inda ‘yancin bauta ke cikin kundin tsarin mulki. Ya kuma kira jama’a da su tallafa wa jami’an tsaro, yana mai tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin ganin an kubutar da ɗaliban da aka sace tare da dawo da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.

Tarayya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Ba Za A Yarda Da Farfado Da Dabi’ar Japan Ta Amfani Da Karfin Soji Ba

Ba Za A Yarda Da Farfado Da Dabi’ar Japan Ta Amfani Da Karfin Soji Ba

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.