ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

by Sulaiman
20 seconds ago
NAHCON

Gwamnatin Jihar Zamfara ta yaba wa Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Alhaji Isma’il Abba Yusuf, bisa nasarar da aka samu wajen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 cikin tsari da nasara.

Wata tawaga daga gwamnatin jihar, ƙarƙashin jagorancin Manajan Daraktan Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Gusau, Alhaji Kabiru Yahaya Gusau, ta kai masa ziyarar girmamawa a ranar Alhamis, 2 ga Yuli, 2026, a Hajj House da ke Abuja domin taya shi murnar kammala aikin Hajjin bana cikin nasara.

Tawagar, wadda Gwamnan Jihar Zamfara, Dakta Dauda Lawal, ya aike, ta haɗa da Daraktan Kuɗi da Kayayyaki, Alhaji Yahuza Mai Haja; Daraktan Fasahar Sadarwa da Bayanai (ICT) na Hukumar Kula da Harajin Cikin Gida ta Jihar Zamfara, Alhaji Bilyaminu Ahmad Muhammed; da kuma Jami’in Haraji, Alhaji Anas Muhammed Gusau.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a madadin tawagar, Alhaji Kabiru Yahaya Gusau ya isar da saƙon godiya daga Gwamna Dauda Lawal ga Shugaban NAHCON.Ya yabawa Jakada Isma’il Abba Yusuf bisa nagartaccen jagoranci, kyakkyawan tsari da ingantacciyar daidaitawa, waɗanda ya ce sun taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da gudanar da aikin Hajjin 2026 cikin nasara.

Har ila yau, tawagar ta nuna gamsuwarta da irin hidimomin da aka samar wa alhazan Nijeriya, tare da yaba kyakkyawar alaƙar aiki tsakanin Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) da Hukumomin Jin Daɗin Alhazai na Jihohi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

A nasa jawabin, Jakada Isma’il Abba Yusuf ya gode wa Gwamna Dauda Lawal da Gwamnatin Jihar Zamfara bisa wannan karamci da girmamawa da suka nuna masa.

Ya bayyana cewa nasarar aikin Hajjin 2026 ba ta taƙaitu gare shi kaɗai ba, illa ta samo asali ne daga haɗin gwiwar ma’aikatan NAHCON, Hukumomin Jin Daɗin Alhazai na Jihohi da sauran masu ruwa da tsaki.

Shugaban ya kuma jaddada aniyar hukumar na ci gaba da inganta ayyukanta da kyautata hidimomin da ake bai wa alhazan Nijeriya.

An kammala ziyarar ne da gudanar da addu’o’in Allah Ya ci gaba da ba Hukumar Alhazai ta Ƙasa nasara a ayyukanta, tare da ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumar da Gwamnatin Jihar Zamfara wajen tafiyar da harkokin aikin Hajji.

NAHCON
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
  • Sulaiman
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
  • Sulaiman
    Sin Ta Soki Abin Da Amurka Da Tarayyar Turai Ke Kira Da Wai ‘Damuwa Kan Sabuwar Dokar Kabilu’
  • Sulaiman
    CGTN Ta Gudanar Da Nazari Kan Yadda Jama’Ar Duniya Ke Kallon Amurka

MASU ALAKA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
Labarai

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
Labarai

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Labarai

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.