Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka (CAF) ta sanar da cewa ta buɗe ƙofa ga ƙasashen nahiyar da ke son ɗaukar nauyin gasar kofin ƙasashen Afirka (AFCON) ta shekarun 2028, 2032 da 2036.
A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na intanet, CAF ta gayyaci dukkanin ƙasashe 54 mambobinta da su gabatar da buƙatarsu ta hanyar da hukumar ta tanada idan suna sha’awar karɓar baƙuncin gasar.
Hukumar ta ce ta fara tsarin zaɓen ƙasashen da za su karɓi baƙuncin AFCON a cikin shekaru 10 masu zuwa.
Ta bayyana cewa hakan na daga cikin ƙoƙarinta na tabbatar da gaskiya da tsari a wajen zaɓen ƙasashen da za su ɗauki nauyin gasar, tare da ƙara ɗaga darajar AFCON a duniya.
CAF ta ce kowace ƙasa mamba na da damar neman ɗaukar nauyin gasar a ɗaya ko sama daga cikin shekarun da aka bayyana.
Sai dai za a tantance ko ƙasar na da filayen wasanni masu inganci da sauran kayayyakin da ake buƙata kafin a ba ta damar shirya gasar.
Sanarwar na zuwa ne yayin da ake shirin gudanar da gasar AFCON ta 2027, wadda ƙasashen Kenya, Tanzania da Uganda za su haɗa hannu wajen karɓar baƙuncinta.
An shirya gudanar da gasar daga ranar 19 ga watan Yuni zuwa 17 ga watan Yuli, 2027.
Wannan ne karon farko da ƙasashe uku na Gabashin Afirka za su haɗa kai wajen ɗaukar nauyin gasar AFCON.














