ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 hours ago
Atiku

Ana gwada kwanji a tsakanini ‘yan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu da Atiku Abubakar da Peter Obi domin samun kuri’u masu rinjaye a yankin Arewacin Nijeriya a lokacin zaben 2027.

A kan wannan ne cacar baki ta kaure a tsakanin tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, da tsohon gwamnan Jihar Borno, Ali Modu Sheriff, na kokarin samun goyon baya a yankin Arewacin Nijeriya.

Sheriff, yayin magana kan sauye-sauyen da ke gabatowa kafin zabin shugaban kasa a wata hira a shirin siyasa ta yau na gidan talabijin na Channels TB, ya ce masu kada kuri’a na Arewa ba za su taba goyon bayan Peter Obi ba. Kwankwaso ya yi watsa da ikirarin, yana jaddada cewa babu wani mutum da ke da hurumin magana a madadin Arewa.

ADVERTISEMENT

Cacar bakin ya zama muhawara a talabijin da sharhi a jaridu da kuma dogon tattaunawa a cikin harkokin siyasa.

Amma masu nazari kan harkokin siyasa a Nijeriya sun gano cewa cacar bakin ba wai game da Peter Obi ko wani dan takara na shugaban kasa ba. Abin yana da zurfi fiye da haka. Wanda, bayan Muhammadu Buhari, mutum zai iya fahimtar cewa ko jan ragamar zuciyar siyasa a Arewacin Nijeriya yana da sauki? Wannan tambaya ce da yanzu take tsakiyar duk wani lissafin zaben 2027. mai mahimmanci.

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Tsawon shekaru masu yawa, ‘yan siyasa sun na magana game da Arewa kamar dai idan dan sayasa ya samu nasara a yanki shi ne zai zama shugaban kasa a duk wani zabe da zai gudana.

Masana harkokin siyasa a Nijeriya sun tabbatar da cewa yankin Arewa yana da matukar tasiyasa a duk wani zabe a Nijeriya.

Zaben 2023, ya nuna karara cewa Arewa tana da tasiri a zaben Nijeriya. Maimakon jama’a su hadu a bayan wani dan takara na Arewa mai rinjaye, masu kada kuri’a sun rarrayabu a jam’iyyu daban-daban na siyasa. Tinubu ya samu babban goyon baya kuma a karshe ya tabbatar da samun shugabancin kasa. Atiku Abubakar ya yi tasiri a sassan Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma. Kwankwaso ya yi nasara a Kano a jam’iyyar NNPP. Peter Obi ya samu nasara a wasu sassan Arewa ta tsakira.

Wannan sauyi ya sa siyasar Arewa ta zama mai bude kofa ga duk dan takarar da ya cancanta.

Yayin da shekarar 2027 ke karatowa, dukkan manyan jam’iyyun siyasa na ganin cewa Arewan Nijeriya har yanzu ita ce wuri mafi muhimmanci na fafatawa.

APC na ganin kasancewa tana da mulki, za ta samu damar kara fadada tasirinta a yanki wanda hakan zai sa samu nasara a zaben 2027. Yayin da ‘yan adawa na cewa kwancin tattalin arziki da rashin tsaro za su haifar da yanayin sauyin siyasa a yankin.

Shin Arewacin Nijeriya ya shiga wani sabon zamani na siyasa ne, wanda babu wani dan siyasa guda daya da zai iya da’awar mallakar yankin. Lokaci ne kawai zai tabbatar da haka.

Atiku
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

MASU ALAKA

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Next Post
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.