Ana gwada kwanji a tsakanini ‘yan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu da Atiku Abubakar da Peter Obi domin samun kuri’u masu rinjaye a yankin Arewacin Nijeriya a lokacin zaben 2027.
A kan wannan ne cacar baki ta kaure a tsakanin tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, da tsohon gwamnan Jihar Borno, Ali Modu Sheriff, na kokarin samun goyon baya a yankin Arewacin Nijeriya.
Sheriff, yayin magana kan sauye-sauyen da ke gabatowa kafin zabin shugaban kasa a wata hira a shirin siyasa ta yau na gidan talabijin na Channels TB, ya ce masu kada kuri’a na Arewa ba za su taba goyon bayan Peter Obi ba. Kwankwaso ya yi watsa da ikirarin, yana jaddada cewa babu wani mutum da ke da hurumin magana a madadin Arewa.
Cacar bakin ya zama muhawara a talabijin da sharhi a jaridu da kuma dogon tattaunawa a cikin harkokin siyasa.
Amma masu nazari kan harkokin siyasa a Nijeriya sun gano cewa cacar bakin ba wai game da Peter Obi ko wani dan takara na shugaban kasa ba. Abin yana da zurfi fiye da haka. Wanda, bayan Muhammadu Buhari, mutum zai iya fahimtar cewa ko jan ragamar zuciyar siyasa a Arewacin Nijeriya yana da sauki? Wannan tambaya ce da yanzu take tsakiyar duk wani lissafin zaben 2027. mai mahimmanci.
Tsawon shekaru masu yawa, ‘yan siyasa sun na magana game da Arewa kamar dai idan dan sayasa ya samu nasara a yanki shi ne zai zama shugaban kasa a duk wani zabe da zai gudana.
Masana harkokin siyasa a Nijeriya sun tabbatar da cewa yankin Arewa yana da matukar tasiyasa a duk wani zabe a Nijeriya.
Zaben 2023, ya nuna karara cewa Arewa tana da tasiri a zaben Nijeriya. Maimakon jama’a su hadu a bayan wani dan takara na Arewa mai rinjaye, masu kada kuri’a sun rarrayabu a jam’iyyu daban-daban na siyasa. Tinubu ya samu babban goyon baya kuma a karshe ya tabbatar da samun shugabancin kasa. Atiku Abubakar ya yi tasiri a sassan Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma. Kwankwaso ya yi nasara a Kano a jam’iyyar NNPP. Peter Obi ya samu nasara a wasu sassan Arewa ta tsakira.
Wannan sauyi ya sa siyasar Arewa ta zama mai bude kofa ga duk dan takarar da ya cancanta.
Yayin da shekarar 2027 ke karatowa, dukkan manyan jam’iyyun siyasa na ganin cewa Arewan Nijeriya har yanzu ita ce wuri mafi muhimmanci na fafatawa.
APC na ganin kasancewa tana da mulki, za ta samu damar kara fadada tasirinta a yanki wanda hakan zai sa samu nasara a zaben 2027. Yayin da ‘yan adawa na cewa kwancin tattalin arziki da rashin tsaro za su haifar da yanayin sauyin siyasa a yankin.
Shin Arewacin Nijeriya ya shiga wani sabon zamani na siyasa ne, wanda babu wani dan siyasa guda daya da zai iya da’awar mallakar yankin. Lokaci ne kawai zai tabbatar da haka.














