ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba

by Umar Faruk and Sulaiman
7 months ago
kebbi

A ranar Litinin ne ‘yan bindiga suka samu nasarar kai hari a Makaratar Sakandare ‘yan mata da ke a garin Maga a karamar hukumar mulki ta Danko Wasagu a Jihar Kebbi, inda Suka yi awon gaba da ‘ya matan guda Ashirin da biyar da kuma harbe wani malami mai suna Malam Hassan Makuku.

Wakilinmu ya samu zanta wa da Matar mariyayin, inda ta bayyana yadda ‘ Yan bindigar Suka Kashe Mijinata yayin da Suka kawo hari a Makaratar Sakandare ta ‘yan mata Kafin samun nasarar yin awon gaba da ‘ya matan. Ta ce” a daren ranar lahadi da misalin karfe 2 zuwa 4 na asuba wayewar safiyar litinin ne ‘yan bingida Suka shigo Makaratar ta Maga, inda Suka fara yada zango a gidanmu a cikin Makaratar, naji alamar motsin bude kofa shigowa gidan sai na tada mijin nawa Malam Hassan Makuku cewa ya tashi ga awaki nan sun bude kofar gida domin kada suyi muna barna, ashe ‘yan bingida ne.

  • Sai An Magance Cin Hanci Da Rashawa Nijeriya Za Ta Zauna Lafiya – Masani
  • Rukunin Ba Da Tallafin Jinya Na Sin Da Asibitin Nijar Sun Gudanar Da Aikin Jinya Kyauta

” Muna tada kai sai kawai muka gan mutane kewaye da mu da bingigoginsu, inda suke sanye da tufafi irin na soje kuma yaren Fulani suke yi. Sai suka cewa maigidana ya gwada musu inda ‘yan Makaratar ke kwana, sai ya basu amsar cewa bai sani ba, daga nan kawai sai daya daga cikinsu ya halba bingigarsa zuwa ga jikin maigidana yayin da naga zai fadi sai na tashi da nufin na tallabe shi, sai suka daka mani tsawa cewa idan na tallaba shi zasu harbe ni.

ADVERTISEMENT

Daga nan sai ban taba shi ba, nima suka cewa sai na shiga gaba in gwada musu inda ‘yan Makaratar ke kwana, muna cikin hakan sai kawai Suka ji tashin yara daga nan sai suka aukawa ‘yan Makaratar, Kafin a samu dauki daga mutane ko jami’an tsaro sun samu nasarar awon gaba da ‘ya matan guda Ashirin da biyar kamar yadda bayyanai Suka nuna a hukumance, Inji Amina Hassan Makuku”.

Bayan an dauki lokaci, sai ga jama’ar gari da jami’an tsaro, Amma a lokacin sun samu nasarar awon gaba da ‘ya matan. Bayan na dawo cikin hayyacina a lokacin ne na iya bada labarin yadda suka harbe Mijina. Kazalika sai ga tawagar mataimakin Gwamna ya shigo Makaratar bayan samu labarin abin da ya faru a Makaratar. Bayan daukar wani lokaci sai kuma maigirma Gwamnan Jihar Daktar Nasir Idris tare da wasu mutane ya shigo, Wanda muka samu labarin cewa ko da wannan matsala ta samu baya a gari yana Abuja, Amma anan take ya shigo jirgi zuwa Makaratar garin Maga don jajanta muna kan irin abin da ya same mu.
Bayan ya kammala zagayawa ya kuma gana damu da sauran uwayen ‘yan makaratar, inda ya tabbatar muna da cewa gwamnati za ta dauki duk matakin da ya dace domin tabbatar da cewa an ceto wannan yaran.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Har ilayau, Amina Hassan Makuku ta kara da cewa” Mijina Malam Hassan Makuku malami ne a wannan Makaratar haka kuma shi ne ke kula da harakokin tsaron Makaratar Kafin ‘yan bingida kuka Kashe shi.
Har ilayau wakilinamu ya zanta da wani mai suna Lawal Altine, mahaifin dalibai uku a makarantar, inda ya ce” muna jiran muji labarin cewa an ceto muna yaranmu matan da ‘yan bingida suka yi awon gaba dasu,In ji shi”. Ya ci gaba da cewa “Daya daga cikin ‘ya’yana mata, Khadija ‘yan aji shida ce, Allah ya tsare ta ta hanyar boyewa a bayan gida. Ta yi sa a, ba ta damu da duk harbe harben da ‘yar bingidar suka yi tayi ba, har sai da suka yi awon gaba da ‘yar uwanta bayan su wuce sannan ta fito dag bayan gida ta bature ke kira toilet, In ji shi “. Wani labarin da nake bayyanawa abin da Khadija ta bayyana ne yayin da mu uwaye muka samu labarin abin da ke faru sannan muka shigo Makaratar.

“Muna cikin tashin hankali da fargaba bisa ga halin da muke ciki a halin yanzu. Amma da yake mai girma Gwamnan Jihar Daktar Nasir Idris ya bamu tabbacin ceto muna yaranmu zamu dan ji dama. In ji shi.
Wani mahaifin, Fatima Ibrahim, ya bayyana cewa “Ina so gwamnati ta taimakamu wajen ganin an gwaggata ceto muna yaranmu tun ‘yan bingida basu hallakasu ba, inji shi.

Saboda haka, muna rokon Allah ya dawo muna da yaranmu cikin koshin lafya ba tare da wata matsala ba.
A nashi jawabi ga uwayen yaran da aka sace, Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, ya ziyarci makarantar kuma ya hadu da iyayen matan da aka sace, ya basu tabbatacin cewa duk abin da zai yiwu za a yi don tabbatar da cewa an ceto wadannan yaran, Inji shi”.

Hukumomin tsaro sun sha alwashi tabbatar da cewa sun gudanar aikin ba dare ba rana don ganin cewa sun ceto wadannan yaran. Hakan kuma za su gudanar da aikin hadin gwiwa tare da ‘yan sanda, sojoji, da kuma jami’an ‘yan banga da aka turo a yankin don tabbatar da cewa an ceto wadannan yaran da aka sace.

Babban Hafsan Sojojin Nijeriya, Janar Waifi Shibu, ya ba da umarni ga jami’an sojoji na tabbatar da sun kara kwazo da inganta kokarinu wajen ganin cewa an ceto ‘yan matan, za mu tabbatar da cewa wadannan ‘yan matan Makaratar Sakandare ta Maga sun dawo ga hannun uwayensu cikin koshin lafiya, In ji shi”.

Al’ummar garin Maga sun faru gudanar da addu’o’i na musamman don ganin cewa Allah karbi addu’arsu don samun nasarar ceto wadannan yaran.

kebbi
Umar Faruk
+ posts Bio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri
kebbi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Gwamnan Neja Ya Yi Allah-Wadai Da Sace Ɗaliban St. Mary A Papiri

Gwamnan Neja Ya Yi Allah-Wadai Da Sace Ɗaliban St. Mary A Papiri

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.