Mai magana da yawun gwamnatin Tanzaniya kuma sakataren dindindin na ma’aikatar watsa labarai, al’adu, fasaha da wasannin motsa jiki Gerson Msigwa, ya yi imanin cewa, a matsayin wani muhimmin sakamako na hadin gwiwa tsakanin Tanzaniya, Sin, da Zambiya, habaka layin dogo na Tanzaniya da Zambiya ba wai kawai zai inganta tsarin sufuri na yankin da inganta karfin ci gaban Tanzaniya da Zambiya ba ne, har ma zai bude sabon babi na hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da kuma habaka ci gaban zamanantarwa a Afirka.
Ya bayyana hakan ne yayin da ya yi wata hira ta musamman da wani dan jarida daga babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG a kwanan nan, game da batun kaddamar da amfani da layin dogo na Tanzaniya da Zambiya da kuma aikin habaka shi. Ya kuma jadadda cewa, a matsayinta na muhimmiyar abokiyar hadin gwiwa a cikin tsarin ci gaban Tanzaniya har ma da Afirka, Sin ta dage kan ka’idojin moriyar juna cikin daidaito, da girmamawa juna, tana taimaka wa kasashen Afirka wajen samun ci gaba da kuma ci gaba da kara kuzari ga bunkasa zamanantarwar Afirka bisa darussa da nasarorin da ta samu yayin bunkasa zamanantarwa iri ta Sin.
Layin dogo na Tanzaniya da Zambiya shi ne layin dogo na farko da gwamnatin Sin ta ba da tallafin ginawa ga waje. An kaddamar da aikin amfani da layin dogon tare da habaka shi a hukumance a watan Nuwamban 2025.(Safiyah Ma)














Discussion about this post