Firaministan Canada Mark Carney, na gab da kawo ziyara kasar Sin daga ranar 14 zuwa na 17 ga watan nan na Janairu. Game da ziyarar, tsohon firaministan Canada Jean Chretein, ya bayyana yayin wata hira cikin shirin “Leaders Talk” na kafar CMG cewa, yana fatan ziyarar za ta zama wani sabon mafari a dangantakar Canada da Sin.
A cewar tsohon firaministan, saboda hargitsin da matakan shugaban Amurka suka haifar, Canada na neman hada gwiwa da sauran kasashe domin bunkasa tatalin arzikinta. Ya ce tattalin arzikin Canada da Sin za su iya marawa juna baya, bisa la’akari da cewa, Sin na da albarkar jama’a yayin da Canada ke da albarkatun fili da kuma kwararru. Don haka, ya ce kasashen biyu za su iya hada gwiwa domin samun ci gaba na bai daya cikin lumana da wadata. (FMM)















Discussion about this post