Kakakin rundunar sojojin ’yantar da jama’ar kasar Sin reshen kudancin kasar, babban kanar Zhai Shichen ya bayyana cewa, daga ranar Alhamis 9 zuwa jiya Lahadi 12 ga watan nan, sojojin ruwa na rundunar ’yantar da jama’ar kasar Sin reshen kudancin kasar, sun gudanar da sintiri a tekun kudancin kasar kamar yadda suka saba.
Zhai ya kuma ce matakin kasar Philippines na hada kai da wasu kasashen da ba na shiyyar ba, wajen gudanar da sintirin hadin gwiwa, ya illata yanayin zaman lafiyar tekun kudancin kasar Sin. Don haka, sojojin rundunar ’yantar da jama’ar kasar Sin reshen kudancin kasar, za su tsaya tsayin daka wajen kare ikon kasar na yankunanta da ma tekunta, tare da kiyaye zaman lafiyar shiyyar. (Lubabatu Lei)














Discussion about this post