Kwamandan Bataliya ta 242 da ke Monguno, Kanal I.A. Mohammed, tare da akalla sojoji 10 sun rasa rayukansu bayan motar su ta taka bam da ake zargin ‘yan ta’adda ne suka dasa akan hanya a karamar hukumar Monguno ta jihar Borno.
Majiyoyin yankin sun bayyana cewa an kashe Kanal Mohammed ne yayin da yake kan hanyar kai dauki bayan wani hari da aka kai sansanin sojoji da daddare.
- Ingila, Faransa Da Ƙasashe 40 Zasu Yi Taron Nemo Mafita Kan Buɗe Mashigar Hormuz
- Nasir El-Rufai Ya Tattauna Taron ADC Yayin Zuwansa Kotu
An ce lamarin ya faru ne lokacin da jami’in ya amsa kiran gaggawa daga sojojin da ake kai wa hari a wani sansani na gaba-gaba (FOB), wanda ke da alaka da Bataliya ta 242.
A cewar majiyoyin, motarsa ta taka bam din IED ne yayin da yake hanzarin zuwa taimakawa FOB, bayan da ake zargin ‘yan ta’adda sun kai musu hari a daren Lahadi.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, wannan lamari ya faru ne kwanaki uku kacal bayan kashe kwamandan Birget na Rundunar Task Force ta 29, Birgediya Janar Oseini Braimah, tare da akalla sojoji 17 da ake zargin ‘yan ta’adda ne suka kashe yayin wani hari a sansanin da ke Benisheikh, karamar hukumar Kaga ta jihar Borno.
Jami’in yada labarai na Rundunar Hadin Gwiwa (Arewa maso Gabas), Operation HADIN KAI, Laftanar Kanal Sani Uba, ya tabbatar da harin, inda ya ce lamarin ya faru ne a daren ranar 12 ga Afrilu, lokacin da sojojin Sashen 3 na rundunar OPHK suka fuskanci wani harin ‘yan ta’adda a wurin Charlie 13 da ke Monguno.
ADVERTISEMENT














Discussion about this post