A yau Talata ne mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng, ya gana da shugaban majalisar dokokin kasar Senegal Malick Ndiaye, a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.
Han Zheng ya bayyana cewa, Senegal abokiyar hadin gwiwa ce mai muhimmanci ga Sin a nahiyar Afirka. Kuma a cikin ‘yan shekarun nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Diakhar Faye, da firaministan Ousmane Sonko yayin ziyararsu a Sin a lokuta daban-daban, inda suka jagoranci ci gaban dangantakar hadin gwiwa ta Sin da Senegal bisa manyan tsare-tsare domin samun sabbin ci gaba.
Han ya kara da cewa, bangaren Sin yana matukar jinjinawa goyon baya, da fahimtar da bangaren Senegal ya bayar kan batutuwa kamar na yankin Taiwan, da hakkin dan Adam, da kuma abubuwan da suka shafi yankin Xinjiang, kana Sin na fatan kara yin hadin gwiwa da bangaren Senegal wajen karfafa amincewar siyasa, da zurfafa hadin gwiwa, kana da karfafa hadin kan manufofin ci gaba, da kara mu’ammalar jama’a, da kuma inganta hadin gwiwa a harkokin kasa da kasa da na yankuna, ta yadda za su bayar da gagarumar gudunmawa ga gina kyakkyawar makomar jama’ar Sin da Afirka ta bai daya a sabon zamani.
A nasa bangaren, mista Ndiaye ya ce Senegal tana tsayawa tsayin daka kan ka’idar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Ya ce bangaren Senegal yana yabawa sosai da shawarar “ziri daya da hanya daya” wadda shugaban kasar Xi ya gabatar, da manyan shawarwari guda hudu na duniya, kuma yana fatan kara hadin kai da bangaren Sin, don karfafa hadin gwiwarsu a fannonin samar da ababen more rayuwa, da sufuri na zamani da sauransu, tare da inganta ci gaban dangantakar nahiyar Afirka da Sin. (Amina Xu)















Discussion about this post