Da safiyar yau Talata 8 ga wata ne mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng, ya halarci bikin bude taron tattaunawa kan zuba jari da kasuwanci na sassan kasa da kasa na kasar Sin, wato CIFIT karo na 26 a birnin Xiamen na lardin Fujian na kasar Sin, inda kuma ya gabatar da jawabi.
A cikin jawabinsa, Han Zheng ya bayyana cewa, sau da dama shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka kan manufar kara bude kofa ga kasashen waje, da sa kaimi ga yin ciniki da zuba jari cikin ‘yanci da sauki.
Ya ce a halin yanzu, duniya ta shiga wani lokaci na tinkarar sabon sauyin yanayi, inda ake kara fuskantar yanayi marar tabbaci, amma duk da haka ba a sauya manufar bude kofa da yin hadin gwiwa ba. Taron CIFIT, ya kasance muhimmin dandalin zurfafa zuba jari da hadin gwiwa na duniya, wanda ke gudana bisa taken dindindin, wato “fadada zuba wa juna jari, da samar da ci gaba ga duniya baki daya”, wanda kuma yake da babbar ma’ana sosai a halin yanzu.
Kazalika, Han Zheng ya bayar da shawarwari uku, wato bukatar bude sabon babi na hadin gwiwa da samun moriyar juna, da gaggauta raya sabbin fannonin samun ci gaba, da kuma tabbatar da hanyoyin samar da kayayyaki yadda ya kamata. (Zainab Zhang)














