Ƙungiyar Paris Saint-Germain (PSG), zakarar Turai ta yanzu, ta samu ‘yan wasa 10 cikin 30 da aka saka cikin jerin waɗanda ke neman lashe kyautar Ballon d’Or ta bana.
Daga cikin ‘yan wasan PSG da aka zaɓa akwai wanda ya lashe kyautar a bara, Ousmane Dembélé, da ɗan wasan tsakiya Vitinha, wanda ya zo na uku a gasar ta bara.
Shahararren ɗan wasan Argentina, Lionel Messi, shi ma yana cikin jerin ‘yan takarar, yayin da yake neman lashe Ballon d’Or karo na tara.
Haka kuma, wanda ya lashe kyautar a shekarar 2024, Rodri, ya dawo cikin jerin ‘yan takarar bayan rawar da ya taka a gasar Kofin Duniya, inda ya lashe kyautar Golden Ball tare da tawagar Spain.
Dan wasa, wanda tauraruwarsa ke haskakawa yanzun, Lamine Yamal da ke kungiyar Barcelona, shima an hange shi cikin sunayen zaɓaɓɓun tare da Sadio Mane, dake kungiyar Al nasr a kasar Saudiyya














