Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa mai ritaya, ya ce fadada damar samun ingantaccen ilimi na daga cikin hanyoyin da suka fi tasiri wajen yaki da ta’addanci da tsattsauran ra’ayi a Nijeriya.
Da yake bayyana matsalolin tsaron Nijeriya a matsayin “yakin ɓuya – wanda da ba a yi ido-da-ido,” ministan ya ce kungiyoyin ’yan ta’adda da masu tsattsauran ra’ayi sukan dogara ne da tsattsauran tunani da yaɗa bayanan karya, wanda hakan ya sanya ilimi zama muhimmin makami wajen dakile tasirinsu.
A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa ministan wajen yada labarai, Leah Katung-Babatunde, ta fitar ranar Litinin, ta ce Musa ya bayyana hakan ne ranar Lahadi yayin kaddamar da wata makaranta mai suna ‘Kaduna Christian Academy’ da ke Ungwan Sunday, Sabon Tasha, a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.
Ministan ya ce, “A matsayina na Ministan Tsaro, ina kallon wannan makaranta a matsayin wata muhimmiyar kadara ta soja ba tare da bindiga ko guda daya ba. Tsaro na gaskiya kuma mai ɗorewa, yana samuwa ne ta hanyar kawar da jahilci da kuma fatattakar rashin fahimta. Wannan makaranta makami ce ta koyarwa mai karfi idan tana hannun waɗanda suka dace.”














Discussion about this post