Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana Legas a matsayin cibiyar tattalin arziƙin Afirka, yana mai cewa birnin ne ya samar da wasu daga cikin manyan attajiran nahiyar tare da ci gaba da zama ginshiƙin tattalin arziƙin Nijeriya.
Da yake jawabi a taron Invest Lagos Summit 3.0 ranar Litinin, Shettima ya ce Legas ta zama muhimmiyar cibiyar zuba jari, ƙirƙire-ƙirƙire da bunƙasar tattalin arziƙi.
Ya ce Legas ta taka muhimmiyar rawa wajen nasarar fitattun ‘yan kasuwa irin su Aliko Dangote da Abdulsamad Rabiu, yana mai cewa damar da suka samu a birnin ce ta taimaka wajen gina kasuwancinsu.
“Legas ce ta samar wa Afirka mutum mafi arziƙi, ba Kano ba. Aliko Dangote mutumin Legas ne,” in ji Shettima, wanda ya ƙara da cewa Abdulsamad ma ya amfana da yanayin kasuwancin da Legas.
Mataimakin Shugaban Ƙasar ya ce Legas ta taimaka wajen gina rayuwar mutane da dama da suka yi fice a Nijeriya, tare da yaba wa jihar kan nagartaccen shugabanci da ci gaba mai ɗorewa.
Ya kuma yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa kafa tubalin ci gaban Legas ta hanyar sauye-sauye da kyakkyawan shugabanci.
A cewarsa, Legas na daga cikin manyan cibiyoyin tattalin arziƙi a Afirka, tana bayar da gudunmawa mai yawa ga GDP na Nijeriya, sannan tana ɗauke da yawancin manyan kamfanonin fasaha na nahiyar.
“Daga cikin kamfanonin unicorn guda tara da ake da su a Afirka, biyar suna Nijeriya kuma duk suna Legas,” in ji shi.














Discussion about this post