Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) a jihar Kebbi ta bayyana cewa jam’iyyun APC da Labour Party (LP) ne kaɗai suka cancanci shiga zaɓen cike gurbi na Majalisar Dokokin jihar da aka shirya gudanarwa ranar 20 ga watan Yuni, 2026, a ƙaramar hukumar Zuru.
Kwamishinan Zaɓe na jihar Kebbi, Abubakar Sarkin Pawa Dambo, ya bayyana hakan yayin wani taro da masu ruwa da tsaki kan shirye-shiryen hukumar na gudanar da zaɓen.
Ya ce INEC ta ware ranakun 22 zuwa 26 ga watan Mayu domin jam’iyyun siyasa su gabatar da sunayen ’yan takararsu kamar yadda sashe na 84 na Dokar Zaɓe ta 2026 ya tanada. Sai dai bayan wa’adin ya ƙare, APC da LP ne kaɗai suka cika ka’idojin INEC wajen gabatar da ’yan takara.
A cewarsa: “Saboda haka, jam’iyyun biyu ne kawai za su shiga zaɓen cike gurbin, kuma ana sa ran za su gabatar da sunayen wakilan rumfunan zaɓensu nan da ranar 10 ga Yuni, 2026.”
Ya ƙara da cewa yakin neman zaɓe zai fara ne a wannan rana kuma zai ƙare ranar 18 ga Yuni, yayin da za a gudanar da zaɓen ranar 20 ga Yuni, 2026.














Discussion about this post