Tsohon Babban Daraktan Gudanarwa na Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), Mele Kyari, ya bayyana cewa ya yi matuƙar mamakin matakin da Kwamitin Kula da Asusun Jama’a na Majalisar Dattawa ya ɗauka na bayar da umarnin kama shi kan binciken da ake yi game da bayanan kuɗaɗen kamfanin.
A cikin wata wasiƙa da ya aike wa shugaban kwamitin, Kyari ya bayyana cewa tun da farko ya sanar da kwamitin rashin yiwuwarsa ta halartar zamansu saboda yana jinya a ƙasar waje.
Ya ce, “Na yi matuƙar mamakin matakin umarnin bayar da sammaci a kaina yayin zaman kwamitinku mai girma a yau, 10 ga Yuni, 2026.”
Kyari ya ƙara da cewa ya sanar da kwamitin a hukumance ta wata wasiƙa mai ɗauke da ranar 11 ga Mayu, 2026, cewa yana karɓar kulawar lafiya a wajen Nijeriya.
A cewarsa, ya kuma bayyana shirinsa na amsa gayyatar kwamitin da zarar ya dawo gida, tare da bayar da damar cewa lauyoyinsa za su iya amsa duk wata tambaya ta gaggawa da kwamitin ke da ita a halin yanzu.
Tsohon shugaban NNPCL ya nuna cewa, bai yi watsi da gayyatar kwamitin ba, sai dai yanayin lafiyarsa ne ya hana shi halarta a lokacin da aka buƙace shi.














Discussion about this post