Babbar Kotun Jihar Kebbi da ke zamanta a Birnin Kebbi ta yanke wa wasu mata uku hukuncin ɗaurin shekaru 14 kowacce bayan samun su da laifin taimaka wa ‘yan bindiga da ke addabar jihar.
Mai shari’a Hassan Shehu Kuwwa ya ce masu gabatar da ƙara sun tabbatar da laifukan haɗa baki, da taimaka wa masu aikata laifi da kuma kasancewa cikin ƙungiyar ‘yan bindiga. Sai dai kotun ta wanke Aisha Abubakar, wadda ita ce ake ƙara da farko, saboda rashin isassun hujjoji.
Matan da aka samu da laifin sun haɗa da Jamila Sule, da Ramatu Habibu da Zara’u Abdulkarim. An same su da laifi ne ƙarƙashin Dokar Penal Code ta Jihar Kebbi ta shekarar 2021.
Kotun ta ji cewa a ranar 14 ga Disamba, 2023, matan sun kai wa ‘yan bindiga da ke dajin Sabon Gari Hills a ƙaramar hukumar Shanga kayan abinci, da abubuwan sha da kuma tabar wiwi. Har ila yau, kotun ta amince da bayanan da aka karɓa daga gare su, waɗanda aka rubuta da Turanci sannan aka fassara zuwa Hausa.
Bayan kammala shari’ar, kotun ta yanke wa Jamila Sule, da Ramatu Habibu da Zara’u Abdulkarim hukuncin ɗaurin shekaru 14 kowacce a gidan yari, yayin da ta sallami Aisha Abubakar tare da wanke ta daga dukkan tuhume-tuhumen da ake mata.














