Tawagar Flying Eagles ta Nijeriya ‘yan ƙasa da shekara 20 ta fara gasar WAFU B ta 2026 da nasara bayan ta doke takwararta ta Ghana, Black Satellites, da ci 4-2 a wasan farko na rukuni na B da aka buga a filin wasa na Charles Konan Banny da ke Yamoussoukro a ƙasar Côte d’Ivoire.
Nijeriya ce ta fara cin ƙwallo ta hannun Olayemi Ayinla a minti na shida, kafin Mohammed Zaidan ya farke wa Ghana a minti na 23. Daga baya Flying Eagles ta ƙara zura ƙwallaye ta hannun Lucky Oraro da Muiz Adeleke, inda ta tabbatar da samun cikakken maki uku a ƙarƙashin jagorancin mai horarwa Aliyu Zubairu.
Da wannan sakamako, Nijeriya ta hau kan teburin rukuni na B, yayin da Ghana ta fara gasar da rashin nasara. Flying Eagles ta nuna ƙwarin gwiwa wajen neman kare kambunta na gasar.
Nijeriya na daga cikin ƙasashen da suka fi samun nasara a gasar matasan Afirka ta ‘yan ƙasa da shekara 20, inda ta lashe kofin sau bakwai. Haka kuma ita ce mai riƙe da kambun WAFU B bayan nasarar da ta samu a gasar shekarar 2022.














