Tawaga ta 27 ta jami’an lafiya ta Sin a Saliyo, ta kaddamar da shirin horar da ma’aikatan jinya ko nas-nas dabarun likitancin gargajiya na Sin, wanda ya hada lakcoci daga masanan Sin ta hanyar na’urori da kuma wadanda jami’an lafiya na Sin da ke kasar za su gabatar kai tsaye, domin karfafa tsarin kiwon lafiya a kasar. Hakika faduwa ta zo dai-dai da zama. Watau yayin da nahiyar Afrika ke fama da yawan al’umma da karancin ci gaba da fasahohi da ma talauci da sauransu, inganta tsarin kiwon lafiya a nahiyar wani babban batu ne da zai taimaka wajen inganta yanayin rayuwar al’umma.
Yawancin lokuta, fargabar tiyata da rashin kudi su ne manyan abubuwan da ke hana mutane zuwa asibiti, amma da likitancin gargajiya irin na Sin da ke mayar da hankali kan gano tushen cuta da maganinta ba tare da tiyata ba, jama’a za su samu kwarin gwiwar zuwa asibiti domin kula da lafiyarsu. Baya ga haka, horar da jami’an lafiya na nufin za su samu wata dabara ta daban, baya ga irin na likitancin yammacin duniya.
Haka zalika, yana nufin za su iya bayar da kulawa ko da babu jami’ai Sinawa. Wannan ma za mu iya bayyana shi da wani misali na yadda Sin ke gabatar da fasahohi da dabarunta ga sauran kasashe maimakon ta yi babakere ko ta kafa shinge.
Bugu da kari, babban misali ne na burin Sin na samar da duniya mai makoma ta bai daya ga dukkan bil adama. Lallai hadin gwiwar Sin da nahiyar Afrika ya cancanci yabo, domin ya zarce batu na tattalin arziki da cinikayya, ya tsallake zancen ababen more rayuwa da musaya, kai tsaye yana taba mutane masu rauni da karamin karfi tare da haifar da sakamako na a zo a gani.
A shekarar 2023 aka cika shekaru 60 da Sin ta fara tura tawagogin jami’an lafiya zuwa ketare, kuma cikin wadannan shekaru 60 da suka gabata, Sin ta tura likitocinta fiye da dubu 30 zuwa kasashe ko yankuna 76, kana yawan mutanen da suka samu jinya kyauta ya kai miliyan 290.
Yanzu haka, akwai tawagogin lafiya na kasar Sin a wurare 115 a kasashe 56 dake fadin duniya, galibinsu wurare ne masu nisa da wahalar rayuwa. Kuma ba duba marasa lafiya kadai suke yi ba, suna aiwatar da tiyata da bayar da horo tare da musayar fasahohi tsakaninsu da dalibai da takwarorinsu likitoci, inda suke barin wani tambari da ba za a iya gogewa ba, domin mutanen da likitocin Sin suka yi jinyarsu, suna ci gaba da tunawa da su tare da yi musu fatan alheri. Wannan ita ce asalin dangantakar abota da ke taba al’umma, da kuma al’umma ke alfahari da ita. (Fa’iza Mustapha)













