ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

by Sulaiman and CGTN Hausa
36 minutes ago
Afrika

Tawaga ta 27 ta jami’an lafiya ta Sin a Saliyo, ta kaddamar da shirin horar da ma’aikatan jinya ko nas-nas dabarun likitancin gargajiya na Sin, wanda ya hada lakcoci daga masanan Sin ta hanyar na’urori da kuma wadanda jami’an lafiya na Sin da ke kasar za su gabatar kai tsaye, domin karfafa tsarin kiwon lafiya a kasar. Hakika faduwa ta zo dai-dai da zama. Watau yayin da nahiyar Afrika ke fama da yawan al’umma da karancin ci gaba da fasahohi da ma talauci da sauransu, inganta tsarin kiwon lafiya a nahiyar wani babban batu ne da zai taimaka wajen inganta yanayin rayuwar al’umma.

Yawancin lokuta, fargabar tiyata da rashin kudi su ne manyan abubuwan da ke hana mutane zuwa asibiti, amma da likitancin gargajiya irin na Sin da ke mayar da hankali kan gano tushen cuta da maganinta ba tare da tiyata ba, jama’a za su samu kwarin gwiwar zuwa asibiti domin kula da lafiyarsu. Baya ga haka, horar da jami’an lafiya na nufin za su samu wata dabara ta daban, baya ga irin na likitancin yammacin duniya.

Haka zalika, yana nufin za su iya bayar da kulawa ko da babu jami’ai Sinawa. Wannan ma za mu iya bayyana shi da wani misali na yadda Sin ke gabatar da fasahohi da dabarunta ga sauran kasashe maimakon ta yi babakere ko ta kafa shinge.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, babban misali ne na burin Sin na samar da duniya mai makoma ta bai daya ga dukkan bil adama. Lallai hadin gwiwar Sin da nahiyar Afrika ya cancanci yabo, domin ya zarce batu na tattalin arziki da cinikayya, ya tsallake zancen ababen more rayuwa da musaya, kai tsaye yana taba mutane masu rauni da karamin karfi tare da haifar da sakamako na a zo a gani.

A shekarar 2023 aka cika shekaru 60 da Sin ta fara tura tawagogin jami’an lafiya zuwa ketare, kuma cikin wadannan shekaru 60 da suka gabata, Sin ta tura likitocinta fiye da dubu 30 zuwa kasashe ko yankuna 76, kana yawan mutanen da suka samu jinya kyauta ya kai miliyan 290.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Yanzu haka, akwai tawagogin lafiya na kasar Sin a wurare 115 a kasashe 56 dake fadin duniya, galibinsu wurare ne masu nisa da wahalar rayuwa. Kuma ba duba marasa lafiya kadai suke yi ba, suna aiwatar da tiyata da bayar da horo tare da musayar fasahohi tsakaninsu da dalibai da takwarorinsu likitoci, inda suke barin wani tambari da ba za a iya gogewa ba, domin mutanen da likitocin Sin suka yi jinyarsu, suna ci gaba da tunawa da su tare da yi musu fatan alheri. Wannan ita ce asalin dangantakar abota da ke taba al’umma, da kuma al’umma ke alfahari da ita. (Fa’iza Mustapha)

Afrika
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”
  • Sulaiman
    Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9
  • Sulaiman
    Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana
  • Sulaiman
    Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil
Afrika
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

MASU ALAKA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi
Ra'ayi Riga

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Afrika

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Afrika

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
Afrika

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.