ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Na Sa Ran Karbar Sauran Kudaden Sallamar Ma’aikatanta Daga CBN Yau Talata – Okoye

by Sulaiman
3 years ago
Okoye

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ƙara jaddada cewa ta na da tabbacin karɓar kuɗaɗen da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi mata alƙawarin bayarwa a yau Talata zuwa gobe Laraba.

 

Kuɗaɗen dai su ne waɗanda za a biya wasu ma’aikatan zirga-zirga ko sufurin da tura masu kuɗaɗe ta asusun ajiyar su zai samu cikas, ɓata lokaci, ko kuma wataƙila ma ba su da asusun ajiyar kwata-kwata.

ADVERTISEMENT
  • INEC Ta Gayyaci ‘Yan Takara Su Sake Rattaba Hannu Kan Zaman Lafiya Ranar Laraba

Kwamishina kuma Babban Jami’in Wayar da Kan Jama’a na hukumar, Festus Okoye, shi ne ya shaida wa manema labarai haka a ranar Lahadi.

 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

INEC ce dai ta roƙi CBN ya tanadar wa hukumar tsabar kuɗaɗe waɗanda za ta biya ayyukan da za ta biya da kuɗi kai-tsaye, ba ta hanyar ‘riransifa’ ba.

 

Da aka tambayi Okoye lokacin da INEC za ta karɓi kuɗaɗen daga CBN, sai ya ce, “Mu na sa ran cewa za mu magance duk wata matsalar biyan kuɗaɗe daga ranar Talata, 21ga Fabrairu.”

 

Okoye ya ce ya na ganin tashe-tashen hankulan ƙone-ƙone da ake yi a wasu garuruwa saboda ƙarancin kuɗaɗe bai zai hana mutane yin tururuwar fita su jefa ƙuri’a ba.

 

Ya ce INEC ta shirya tsaf domin gudanar da zaɓe sahihi kuma karɓaɓɓe, haka ya ke da yaƙinin cewa ɓangarorin tsaro su ma sun yi na su shirin domin samar da kyakkyawan tsaro a lokacin zaɓe da kuma lokacin tattara sakamakon zaɓe da kuma lokacin bayyana sakamakon zaɓe.

 

Makonni biyu da su ka gabata ne shugaban INEC ya kai ziyara a Hedikwatar CBN, inda Gwamnan bankin, Godwin Emefiele, ya cire masa shakkun samun tangarɗar kuɗaɗen sallamar ma’aikatan zaɓe.

 

A lokacin ziyarar, CBN ya shaida wa Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, Farfesa Mahmood Yakubu, cewa sauya launin kuɗi ba zai shafi zaɓen 2023 ba.

 

Ya ce CBN zai samar wa INEC dukkan kuɗaɗen da hukumar ke buƙata a lokacin zaɓukan ranar 25 ga Fabrairu da na 11 ga Maris, 2023.

 

Emefiele ya shaida wa Yakubu cewa a ko da yaushe CBN na goyon bayan INEC ta kowane fanni domin tabbatar da cewa ta gudanar da aikin da aka ɗora wa hukumar a cikin nasara.

 

Ya ce: “Mu na shiga harkokin ayyukan INEC adanawa da ajiyar kayan zaɓe, har ma da amfani da motocin CBN masu sulke wajen rarraba kayan zaɓe.

 

“Mu na farin cikin cewa a cikin wannan kyakkyawar alaƙa tsakanin CBN da INEC, ba mu taɓa kawo wa INEC cikas ko dagula masu lissafi ba. Saboda haka ɗin ne ma ba ku gudun mu, ga shi a yanzu ma kun dawo mana a wannan zaɓen.

 

“Idan shugaban INEC zai tuna, lokacin da na kai maka ziyara a baya, ka tambayi yadda CBN zai samar wa INEC kuɗaɗen waje domin sayen na’urar tantance masu rajistar zaɓe (BVAS), da sauran kayan aikin zaɓe. Na ba ka tabbacin za a samar, kuma an samar ɗin.

 

“Saboda haka CBN ba zai bari a yi amfani da shi ba wajen kawo wa zaɓen 2023 cikas.

 

“Don haka ina tabbatar maka idan ka na buƙatar takardun kuɗaɗe domin biyan motocin sufuri kuɗin su a hannu, bayan ka yi biya ta tiransifa, to CBN a shirye ya ke ya bayar.”

 

Tun da farko, Yakubu ya nemi haɗin kan CBN domin tabbatar da zaɓen 2023 cikin nasara, musamman ganin yadda ake ta haƙilon ƙarancin kuɗaɗe kusa da zaɓe.

 

Yakubu ya ce INEC ta yi shiri tsaf domin tabbatar da zaɓen 2023 ya zama sahihin zaɓen da a tarihi ba a taɓa yin kamar sa ba a Nijeriya.

Okoye
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
BUK Ta Kori Dalibai 27, Ta Dakatar Da 8 Kan Satar Jarabawa

BUK Ta Kori Dalibai 27, Ta Dakatar Da 8 Kan Satar Jarabawa

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.