ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Na Sa Ran Karbar Sauran Kudaden Sallamar Ma’aikatanta Daga CBN Yau Talata – Okoye

by Sulaiman
3 years ago
Okoye

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ƙara jaddada cewa ta na da tabbacin karɓar kuɗaɗen da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi mata alƙawarin bayarwa a yau Talata zuwa gobe Laraba.

 

Kuɗaɗen dai su ne waɗanda za a biya wasu ma’aikatan zirga-zirga ko sufurin da tura masu kuɗaɗe ta asusun ajiyar su zai samu cikas, ɓata lokaci, ko kuma wataƙila ma ba su da asusun ajiyar kwata-kwata.

ADVERTISEMENT
  • INEC Ta Gayyaci ‘Yan Takara Su Sake Rattaba Hannu Kan Zaman Lafiya Ranar Laraba

Kwamishina kuma Babban Jami’in Wayar da Kan Jama’a na hukumar, Festus Okoye, shi ne ya shaida wa manema labarai haka a ranar Lahadi.

 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

INEC ce dai ta roƙi CBN ya tanadar wa hukumar tsabar kuɗaɗe waɗanda za ta biya ayyukan da za ta biya da kuɗi kai-tsaye, ba ta hanyar ‘riransifa’ ba.

 

Da aka tambayi Okoye lokacin da INEC za ta karɓi kuɗaɗen daga CBN, sai ya ce, “Mu na sa ran cewa za mu magance duk wata matsalar biyan kuɗaɗe daga ranar Talata, 21ga Fabrairu.”

 

Okoye ya ce ya na ganin tashe-tashen hankulan ƙone-ƙone da ake yi a wasu garuruwa saboda ƙarancin kuɗaɗe bai zai hana mutane yin tururuwar fita su jefa ƙuri’a ba.

 

Ya ce INEC ta shirya tsaf domin gudanar da zaɓe sahihi kuma karɓaɓɓe, haka ya ke da yaƙinin cewa ɓangarorin tsaro su ma sun yi na su shirin domin samar da kyakkyawan tsaro a lokacin zaɓe da kuma lokacin tattara sakamakon zaɓe da kuma lokacin bayyana sakamakon zaɓe.

 

Makonni biyu da su ka gabata ne shugaban INEC ya kai ziyara a Hedikwatar CBN, inda Gwamnan bankin, Godwin Emefiele, ya cire masa shakkun samun tangarɗar kuɗaɗen sallamar ma’aikatan zaɓe.

 

A lokacin ziyarar, CBN ya shaida wa Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, Farfesa Mahmood Yakubu, cewa sauya launin kuɗi ba zai shafi zaɓen 2023 ba.

 

Ya ce CBN zai samar wa INEC dukkan kuɗaɗen da hukumar ke buƙata a lokacin zaɓukan ranar 25 ga Fabrairu da na 11 ga Maris, 2023.

 

Emefiele ya shaida wa Yakubu cewa a ko da yaushe CBN na goyon bayan INEC ta kowane fanni domin tabbatar da cewa ta gudanar da aikin da aka ɗora wa hukumar a cikin nasara.

 

Ya ce: “Mu na shiga harkokin ayyukan INEC adanawa da ajiyar kayan zaɓe, har ma da amfani da motocin CBN masu sulke wajen rarraba kayan zaɓe.

 

“Mu na farin cikin cewa a cikin wannan kyakkyawar alaƙa tsakanin CBN da INEC, ba mu taɓa kawo wa INEC cikas ko dagula masu lissafi ba. Saboda haka ɗin ne ma ba ku gudun mu, ga shi a yanzu ma kun dawo mana a wannan zaɓen.

 

“Idan shugaban INEC zai tuna, lokacin da na kai maka ziyara a baya, ka tambayi yadda CBN zai samar wa INEC kuɗaɗen waje domin sayen na’urar tantance masu rajistar zaɓe (BVAS), da sauran kayan aikin zaɓe. Na ba ka tabbacin za a samar, kuma an samar ɗin.

 

“Saboda haka CBN ba zai bari a yi amfani da shi ba wajen kawo wa zaɓen 2023 cikas.

 

“Don haka ina tabbatar maka idan ka na buƙatar takardun kuɗaɗe domin biyan motocin sufuri kuɗin su a hannu, bayan ka yi biya ta tiransifa, to CBN a shirye ya ke ya bayar.”

 

Tun da farko, Yakubu ya nemi haɗin kan CBN domin tabbatar da zaɓen 2023 cikin nasara, musamman ganin yadda ake ta haƙilon ƙarancin kuɗaɗe kusa da zaɓe.

 

Yakubu ya ce INEC ta yi shiri tsaf domin tabbatar da zaɓen 2023 ya zama sahihin zaɓen da a tarihi ba a taɓa yin kamar sa ba a Nijeriya.

Okoye
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
BUK Ta Kori Dalibai 27, Ta Dakatar Da 8 Kan Satar Jarabawa

BUK Ta Kori Dalibai 27, Ta Dakatar Da 8 Kan Satar Jarabawa

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.