Dakarun Shiyya 2 na rundunar ‘Operation FANSAN YAMMA’ sun kwato dabbobi 147 da aka sace tare da babura uku a wani samamen yaƙi da ta’addanci da suka gudanar a Ƙaramar Hukumar Shagari ta Jihar Sokoto.
Rundunar Haɗin Gwiwa ta bayyana cewa an samu nasarar kwato dabbobin ne a ranar Talata bayan samun bayanan sirri cewa wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne na wucewa da dabbobin da suka sace ta wasu ƙauyuka da ke yankin.Bisa wannan bayani, dakarun sun yi kwanton ɓauna a wata mashigar a ƙauyen Horo Birni, inda suka tare hanyar maharan.
Sanarwar ta ce, yayin da maharan suka hango dakarun, sai suka yi watsi da dabbobin tare da tserewa cikin daji, suna amfani da mawuyacin yanayin yankin domin guje wa kama su.
Binciken da aka ci gaba da yi a yankin ya kai ga kwato shanu 101, tumaki 44, rakuma biyu da babura uku, waɗanda ake zargin ‘yan ta’addan ke amfani da su wajen gudanar da hare-harensu da zirga-zirga.
Mukaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na Rundunar Haɗin Gwiwa, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba cewa an tantance masu mallakar dabbobin, kuma an miƙa su ga masu su na hakika.














