A karshen makon da ya gabata ne aka gudanar da taron kolin kungiyar BRICS ta kasashe maso saurin samun ci gaba, a birnin New Delhi na kasar India. Yayin taron a ranar Asabar, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabi, wanda ya yi kira ga kungiyar da ta mayar da hankali kan wasu muhimman batutuwa 4.
Da farko dai, babban sakon dake tattare da taron shi ne, kasashe masu tasowa su tashi daga wadanda ake juyawa, zuwa wadanda ake damawa da su cikin harkokin duniya. Watau su sauya daga masu karba ko wadanda ake ba umarni da kakaba wa ka’idoji da dokoki, zuwa wadanda ke da karfin fada a ji, inda su ma za su rika shiga cikin harkokin shugabantar duniya da tafiyar da harkoki da samun ci gaba da tafiyar da harkokinsu na cikin gida da kansu.
Tasirin kungiyar BRICS na karuwa a duniya la’akari da yadda kasashen kungiyar suka dauki kaso 40 na alkaluman GDP na duniya da kaso 49.5 na al’ummar duniya.
Idan muka nazarci batutuwa 4 da shugaban kasar Sin ya gabatar, to a dunkule, mafita ce ga matsalolin da duniya ke fuskanta.Shugaba Xi ya bukaci su zama jagororin samar da ci gaba ta hanyar kirkire-kirkire. Yanayin duniya ya sauya zuwa fasahar zamani, don haka, ya kamata kasashen su tashi tsaye su jagoranci bangaren domin kada a bar su a baya. Idan suka kasance masu tsayawa da kafarsu a bangaren, to za su amfani duniya da jama’arsu, haka kuma za su sauya salon duniya na danniya da babakere.Na biyu ya bukaci su jagoranci tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Tsarin huldar BRICS shi ne girmama juna da hadin gwiwa bisa adalci da daidaito, wanda wata ingantacciyar hanya ce ta tabbatar da zaman lafiya, sabanin tsohon tsarin yammacin duniya na fin karfi da cin zali, wanda ke haifar da tashe-tashen hankula. Akwai bukatar kasashen masu tasiri a duniya, su tsaya kai da fata wajen adawa da cin zali domin a samu duniya mai zaman lafiya da kwanciyar hankali.Na uku, su zama masu bunkasa koyi da juna tsakanin mabambantan al’ummomi.
Fahimtar juna na da matukar muhimmanci wajen wanzar da zaman lafiya tsakanin kasa da kasa. Ba za a samu fahimtar juna ba, har sai an yi mu’amala, an gane al’adu da mabambantan halayyar juna. Wannan shi zai yi maganin masu yada karairayi da jita-jita da dakile gadon adawa tsakanin mabambantan al’ummomi. Na hudu, su jagoranci inganta tsarin shugabancin duniya.
Tabbas idan muka duba tafarkin da ake kai yanzu, to wasu ’yan tsiraru masu arziki ne ke juya duniya bisa son ransu. Sai dai, yanzu akwai tarin kasashe masu tasowa, kuma kan duniya ya waye. Kowacce kasa na da yanayin da ya dace da ita da ya bambanta da na sauran. Don haka, akwai bukatar sauya tsarin shugabancin duniya ta yadda za a samu rarrabuwar iko tsakanin kasa da kasa da kara kyautata mu’amala tsakanin kasashe, maimakon kafa wasu kananan rukunoni, domin kara dunkule tattalin arzikin duniya.
Makomar dukkan dan adam hade suke da juna. Babu kasar da za ta iya ware kanta kuma ta samu ci gaban da take bukata, don haka jawabin na shugaba Xi, da manufofi da burikan kungiyar BRICS, su ne za su kawo mafita ga matsalolin da ake fuskanta da kuma samar da alkiblar wanzar da ci gaba da zaman lafiya da daidaito a duniya. (Faeza Mustapha)













