Ministan kiwon lafiya na kasar Sin Lei Haichao, ya ce kasarsa za ta ci gaba da matsa kaimin samar da karin kyakkyawan yanayi na haihuwar yara, ta hanyar fadada damar reno da hidimomin kiwon lafiyar yara masu rahusa.
Lei Haichao, wanda ya bayyana hakan a Litinin din nan, yayin ganawa da manema labarai a ofishin majalisar gudanarwar kasar Sin, ya ce Sin za ta yayata hadadden tsarin bunkasa hidimomin renon yara da na karatu gabanin fara ilimin firamare.
Ya ce za a karfafa gwiwar al’ummu, da masu daukar ma’aikata wajen samar da abubuwan bukata domin renon yara kanana, ta yadda wadannan hidimomi za su zamo masu karin araha da saukin samu ga iyalai, tare da kara damar cin gajiyarsu, da rage tsadar kudaden reno da na ilmantar da yara.
Lei, ya kara da cewa a shekarar nan ta 2026, Sin za ta samar da karin cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko, da asibitocin garuruwa sama da 1,000 wadanda za su rika samar da hidimomin kiwon lafiyar yara.
Kazalika, ya zuwa karshen shekarar ta 2026, sama da kaso 95 na asibitocin garuruwa, da cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko za su rika samar da hidimomin kiwon lafiyar yara. (Saminu Alhassan)














