Tsohon Shugaban Ƙasar Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya ce Nijeriya ba ta da wani dalili da zai sa ta kasance cikin talauci, yana mai cewa ƙasar na da albarkatun ƙasa da na ɗan Adam da za su iya samar da wadatar da ake buƙata.
Obasanjo ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da shirin C-Suite Cafe, wanda Ikem Okuhu ya jagoranta. Ya ce Nijeriya na da ƙasa, da ruwa, da ruwan sama da ƙwararrun mutane da za su iya samar da isasshen abinci da kuma haifar da arziƙi.
Tsohon shugaban ƙasar ya ce ɗaya daga cikin matsalolin Nijeriya ita ce manufofin da ke fifita shigo da kayayyaki daga ƙasashen waje maimakon ƙarfafa samar da su a cikin gida. Ya bayar da misalin Guinea-Bissau, inda ya ce duk da yawan albarkatun noma da ’ya’yan itatuwa da ake samu a ƙasar, har yanzu ana dogaro da shigo da abinci.
Obasanjo ya kuma tuna da matakin da Nijeriya ta ɗauka a shekarar 1979 na takaita shigo da shinkafa domin ƙarfafa wa manoman cikin gida. A cewarsa, jami’an noma sun tabbatar a lokacin cewa ƙasar na turbar cimma dogaro da kanta wajen samar da shinkafa, amma gwamnatocin da suka biyo baya sun sauya manufar tare da sake ba da damar shigo da shinkafa, lamarin da ya raunana masu noman cikin gida.
Ya jaddada cewa Nijeriya da sauran ƙasashen Afirka na buƙatar amfani da damar da suke da ita wajen noma da sauran albarkatu, tare da rage dogaro da kayayyakin da ake shigowa da su daga ƙasashen waje domin ƙara samar da arziƙi da rage talauci.














