Gwamnatin Jihar Neja ta kammala jigilar maniyyata 2,281 domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 zuwa ƙasar Saudiyya.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta jihar, Yunusa Saidu-Ibrahim, ya fitar a ranar Litinin.
Ya ce, Alhazan sun tashi ne daga Filin Jirgin Sama na Bola Tinubu da ke Minna.
An kwashe maniyyatan, waɗanda suka fito daga ƙananan hukumomi 25 na jihar, zuwa Masarautar Saudiyya cikin jirage shida da Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Neja ta tsara tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin da abin ya shafa.
Gwamnan jihar, Umaru Bago, ya bayyana nasarar kammala jigilar a matsayin sakamakon kyakkyawar haɗin gwiwa, ingantaccen tsari, aiki tukuru, jajircewa da sadaukarwa daga gwamnatin jihar da Hukumar Jin Daɗin Alhazai da sauran hukumomin da suka shiga aikin.
Ya kuma yaba wa Amirul Hajj na shekarar 2026 kuma Sarkin Agaie, Alhaji Yusuf Nuhu, bisa jagoranci da shawarwarin da ya bayar a duk tsawon aikin.















Discussion about this post