Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da belin tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.
Kotun ta bayar da belin ne kan kuɗi naira miliyan 100 tare da sharadin samun mutum guda da zai tsaya masa.
Mai shari’a Joyce Abdulmalik ta gindaya tsauraran sharuɗɗa domin samun belin, inda ta ce dole ne wanda zai tsaya masa ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro a Abuja, sannan ya miƙa asalin takardar mallakar fili ko gida ga kotun.
Kotun ta kuma umurci cewa wanda zai tsaya masa dole ne ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai mataki na 17 ko sama da haka, tare da gabatar da shaidar albashin akalla watanni uku.
Bugu da ƙari, wanda zai tsaya masa zai gabatar da rantsuwar bayyana kadarori, ya sanya hannu kan takardar beli, sannan ya kawo sabon hoton fasfo, wasiƙar tabbatarwa daga ma’aikatarsa da kuma takardar biyan haraji ta watanni shida da suka gabata.
Kotun ta kuma umurci El-Rufai da ya miƙa duk wasu fasfo na ƙasa da ƙasa masu aiki da yake da su.
Mai shari’a Abdulmalik ta ƙara da umartar sa da riƙa kai rahoto hedikwatar Hukumar DSS a kowace Juma’a ta ƙarshen wata da ƙarfe 10 na safe domin sanya hannu a rajistar halarta har sai an kammala shari’ar.
Kotun ta yi gargaɗin cewa karya wa ko saɓa wa duk wani daga cikin sharuɗɗan zai sa a soke belin kai tsaye.
An gurfanar da tsohon gwamnan ne kan zargin sa ido ko satar bayanan wayar mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Nuhu Ribadu.













Discussion about this post